< Ishaya 55 >
1 “Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
Nu vel! hver den, som tørster, komme hid til Vandene, og I, som ikke have Penge, komme hid, køber og æder; kommer, køber uden Penge og uden Betaling Vin og Mælk!
2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
Hvi veje I Penge ud, for hvad der ikke er Brød, og eders Dagløn, for hvad der ikke kan mætte? hører dog paa mig og æder det gode, saa skal eders Sjæl kvæge sig med det fede.
3 Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
Bøjer eders Øre og kommer hid til mig, hører, saa skal eders Sjæl leve; thi jeg vil gøre en evig Pagt med eder, paa de trofaste Forjættelser til David.
4 Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
Se, jeg har sat ham til et Vidne for Folk, til en Fyrste og til en Hersker over Folkeslag.
5 Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Se, du skal kalde ad et Folk, som du ikke kender, og et Folk, som ikke kender dig, skal ile til dig, for Herren din Guds Skyld og for Israels Helliges Skyld; thi han har herliggjort dig.
6 Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
Søger Herren, medens han findes, kalder paa ham, medens han er nær.
7 Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
Den ugudelige forlade sin Vej og den uretfærdige sine Tanker og omvende sig til Herren, saa skal han forbarme sig over ham, og til vor Gud; thi han er meget rund til at forlade.
8 “Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
Thi mine Tanker ere ikke eders Tanker, og eders Veje ere ikke mine Veje, siger Herren.
9 “Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
Thi som Himmelen er højere end Jorden, saa ere mine Veje højere end eders Veje og mine Tanker højere end eders Tanker.
10 Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
Thi ligesom Regnen og Sneen nedfalder fra Himmelen og vender ikke tilbage derhen, men vander Jorden og gør den frugtbar og kommer den til at give Grøde og frembringer Sæd til at saa og Brød til at æde:
11 haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
Saa skal mit Ord være, som udgaar af min Mund, idet skal ikke komme tomt tilbage til mig; men det skal gøre, hvad mig behager, og det skal have Lykke i, hvad jeg sender det til.
12 Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
Thi I skulle drage ud med Glæde og føres frem i Fred; Bjergene og Højene skulle raabe for eders Ansigt med Frydesang, og alle Træer paa Marken skulle klappe i Haand.
13 A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”
I Stedet for Tornebuske skal der opvokse Fyrretræer, i Stedet for Tidsler skal der opvokse Myrtetræer; og det skal være Herren til et Navn, til et evigt Tegn, som ikke skal forgaa.