< Ishaya 54 >
1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
Jubla, du ofruktsamma, du som icke har fött barn; brist ut i jubel och ropa av fröjd, du som icke har blivit moder. Ty den ensamma skall hava många barn, flera än den som har man, säger HERREN.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Vidga ut platsen för ditt tjäll, låt spänna ut tältet, under vilket du bor, och spar icke; förläng dina tältstreck och gör dina tältpluggar fastare.
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Ty du skall utbreda dig både åt höger och vänster, och dina avkomlingar skola taga hedningarnas länder i besittning och åter befolka ödelagda städer.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
Frukta icke, ty du skall ej komma på skam; blygs icke, ty du skall ej varda utskämd. Nej, du skall få förgäta din ungdoms skam, och ditt änkestånds smälek skall du icke mer komma ihåg.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Ty den som har skapat dig är din man, han vilkens namn är HERREN Sebaot; och Israels Helige är din förlossare, han som kallas hela jordens Gud.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
Ty såsom en övergiven kvinna i hjärtesorg kallades du av HERREN. Sin ungdomsbrud, vill någon förskjuta henne? säger din Gud.
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
Ett litet ögonblick övergav jag dig, men i stor barmhärtighet vill jag åter församla dig.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
I min förtörnelses översvall dolde jag ett ögonblick mitt ansikte för dig, men med evig nåd vill jag nu förbarma mig över dig, säger HERREN, din förlossare.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
Ty såsom jag gjorde vid Noas flod, så gör jag ock nu: såsom jag då svor, att Noas flod icke mer skulle komma över jorden, så svär jag ock nu, att jag icke mer skall förtörnas på dig eller näpsa dig.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Ja, om än bergen vika bort och höjderna vackla, så skall min nåd icke vika ifrån dig och mitt fridsförbund icke vackla, säger HERREN; din förbarmare.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
Du arma, som har blivit så hemsökt av stormar utan att få någon tröst, se, med spetsglans vill jag nu mura dina stenar och giva dig grundvalar av safirer,
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
jag vill göra dina tinnar av rubiner och dina portar av kristall och hela din ringmur av ädla stenar.
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Och dina barn skola alla bliva HERRENS lärjungar, och stor frid skola dina barn då hava.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Genom rättfärdighet skall du bliva befäst. All tanke på förtryck vare fjärran ifrån dig, ty du skall intet hava att frukta, och all tanke på fördärv, ty sådant skall icke nalkas dig.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Om man då rotar sig samman till anfall, så kommer det ingalunda från mig; och vilka de än äro, som rota sig samman mot dig, så skola de falla för dig.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
Se, jag är den som skapar smeden, vilken blåser upp kolelden och så frambringar ett vapen, sådant han vill göra det; men jag är ock den som skapar fördärvaren, vilken förstör det.
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
Och nu skall intet vapen, som smides mot dig, hava någon lycka; var tunga, som upphäver sig för att gå till rätta med dig, skall du få domfälld. Detta är HERRENS tjänares arvedel, den rätt de skola undfå av mig, säger HERREN.