< Ishaya 54 >

1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
ای اورشلیم، ای زن نازا، شاد باش و سرود بخوان، زیرا فرزندان تو زیادتر از فرزندان زنی خواهند شد که شوهرش او را ترک نگفته باشد!
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
خیمه‌ای را که در آن زندگی می‌کنی وسیعتر کن و پرده‌های آن را پهنتر ساز، طنابهایش را دراز کن و میخهایش را محکم ساز؛
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
زیرا به‌زودی جمعیت تو زیاد خواهد شد. فرزندانت نزد تو باز خواهند گشت و این سرزمین را که به دست بیگانگان افتاده، تصاحب خواهند کرد و شهرهای ویران را دوباره آباد خواهند ساخت.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
نترس و نگران نباش، زیرا دیگر رسوا و خوار نخواهی شد. خیانتی را که در جوانیت مرتکب شده‌ای به یاد نخواهی آورد و تنهایی زمان بیوگی‌ات را فراموش خواهی کرد؛
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
زیرا آفرینندهٔ تو که نامش خداوند لشکرهای آسمان است، شوهر تو خواهد بود. خدای قدوس اسرائیل که خدای تمام جهان است، نجا‌ت‌دهندۀ تو خواهد بود.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
ای اسرائیل، تو مانند زن جوان رنجدیده‌ای هستی که شوهرش او را ترک گفته باشد. اما خداوند تو را دوباره نزد خود می‌خواند و می‌گوید:
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
«برای اندک زمانی تو را ترک گفتم، اما اینک با محبتی عمیق تو را نزد خود برمی‌گردانم.»
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
خداوند که حامی توست می‌فرماید: «در لحظهٔ غضب، روی خود را از تو برگردانیدم، اما اینک با محبت جاودانی تو را دوست خواهم داشت.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
«همان‌گونه که در زمان نوح قسم خوردم که دیگر نگذارم طوفان جهان را فرا گیرد، اکنون نیز قسم می‌خورم که بار دیگر بر تو خشمگین نشوم و تو را تنبیه نکنم.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
هر چند کوهها جابه‌جا شوند و تپه‌ها نابود گردند، اما محبت من نسبت به تو هرگز از بین نخواهد رفت و پیمان سلامتی‌ای که با تو بسته‌ام هیچوقت شکسته نخواهد شد.» خداوند که تو را دوست دارد این را می‌گوید.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
«ای شهر داغدیده و رنجور من که تسلی نیافته‌ای، من تو را بازسازی خواهم کرد؛ تو را با سنگهای قیمتی بنیاد خواهم نهاد.
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
برجهایت را با لعل و دروازه‌ها و دیوارهایت را با گوهرهای درخشان بنا خواهم کرد.
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
همهٔ فرزندانت از من تعلیم خواهند گرفت و سلامتی و کامیابی روز افزونی نصیب ایشان خواهد شد.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
عدل و انصاف در تو حکمفرما خواهد شد و تو از ظلم و آزار دیگران در امان خواهی ماند. در صلح و آرامش به سر خواهی برد و دیگر نخواهی ترسید.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
اگر قومی بر تو هجوم آورند، این امر با اجازهٔ من نخواهد بود. پس آنانی که با تو بجنگند، از پای در خواهند آمد.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
«آهنگر را که آتش کوره را می‌دمد و اسلحه می‌سازد، من آفریده‌ام. سرباز را نیز که اسلحه به دست می‌گیرد و می‌جنگد، من به وجود آورده‌ام؛
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
و من می‌گویم هر اسلحه‌ای که بر ضد تو ساخته شود کاری از پیش نخواهد برد و تو بر تمام مدعیانت غالب خواهی شد. من خدمتگزارانم را حمایت می‌کنم و به آنان پیروزی می‌بخشم.» این است آنچه خداوند می‌فرماید.

< Ishaya 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark