< Ishaya 54 >

1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
“Hlabela wena mfazi oyinyumba, wena ongazange uzale umntwana; susa ingoma, umemeze ngentokozo, wena ongakaze uhelelwe ngoba abantwana bomfazi olahliweyo banengi kulabalowo olendoda,” kutsho uThixo.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Qhelisa indawo yethente lakho, yelula amakhetheni ethente lakho abe banzi, ungathikazi, yelula izintambo zakho, uqinise izikhonkwane zakho.
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Ngoba uzaqhela usiya kwesokudla lesenxele; inzalo yakho izazixotsha izizwe yakhe emadolobheni azo adilikayo.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
“Ungesabi, ngoba awuyikwehlelwa lihlazo. Ungesabi ukuyangeka, ngoba awuyikudumazeka. Uzalikhohlwa ihlazo lasebutsheni bakho, ungakhumbuli lesithuko sobufelokazi bakho.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Ngoba uMenzi wakho engumyeni wakho, uThixo uSomandla libizo lakhe oNgcwele ka-Israyeli unguMhlengi wakho; ubizwa ngokuthi nguNkulunkulu womhlaba wonke.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
UThixo uzakubiza njengowesifazane olahliweyo, odabukileyo emoyeni, owesifazane owenda esesemncane, waphanga waliwa,” kutsho uNkulunkulu wakho.
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
“Ngakutshiya okomzuzwana omncane, kodwa ngesihawu esikhulu ngizakubuyisa.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
Ngomfutho wokuthukuthela, ngakufihlela ubuso bami okomzuzwana, kodwa ngothando olungapheliyo, ngizakuba lesihawu kuwe,” kutsho uThixo uMhlengi wakho.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
“Kimi lokhu kunjengasezinsukwini zikaNowa, lapho engafunga khona ngathi amanzi kaNowa kawayikugcwala umhlaba futhi. Ngakho khathesi sengifungile ngathi angiyikukuthukuthelela futhi; angiyikukusola njalo.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Lanxa izintaba zinganyikinyiswa, lamaqaqa asuswe, kodwa uthando lwami olungapheliyo kuwe kaluyikunyikinyiswa, kumbe isivumelwano sami sokuthula sisuswe,” kutsho uThixo olesihawu kuwe.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
Wena dolobho elihluphekileyo, elitshaywa yiziphepho alaze laduduzwa, ngizakwakha ngamatshe amahle, izisekelo zakho ngizakhe ngamasafire.
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
Izakhiwo zakho zokuvikela ngizazenza ngamarubhi, amasango akho ngiwenze ngamatshe akhazimulayo, yonke imithangala yakho ngiyenze ngamatshe aligugu.
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Wonke amadodana akho azafundiswa nguThixo, njalo kuzakuba kukhulu ukuthula kwabantwana bakho.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Uzaqiniswa ngokulunga: uchuku luzakuba khatshana lawe, awuyikwesaba lutho. Ukwesaba kuzasuselwa khatshana, akuyikusondela phansi kwakho.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Nxa ekhona ozakuhlasela, kobe kungayisimi; loba ngubani okuhlaselayo uzazinikela kuwe.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
“Khangela, yimi engadala umkhandi wensimbi ovuthela amalahle abe lilangabi, akhande isikhali esilungele umsebenzi waso. Njalo yimi engadala umchithi ukuba enze umonakalo;
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
akulasikhali esikhandelwe wena esizaphumelela, njalo bonke abakumangalelayo uzabehlula. Leli yilifa lezinceku zikaThixo, lokhu yikho ukwenaniswa kwazo yimi,” kutsho uThixo.

< Ishaya 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark