< Ishaya 54 >

1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
Yerusalem, dahulu engkau seperti wanita mandul yang tak bisa melahirkan. Tetapi sekarang bersorak-soraklah, dan bernyanyilah dengan gembira! Sebab anak-anakmu banyak sekali, melebihi anak wanita yang tidak ditinggalkan suami.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Luaskanlah kemah-kemah kediamanmu; panjangkan tali-talinya dan kokohkan pasak-pasaknya!
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Engkau akan bertambah luas ke kanan dan kiri, pendudukmu akan menduduki tanah bangsa-bangsa dan mendiami kota-kota yang sekarang sunyi sepi.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
Jangan takut, engkau tak akan dipermalukan; tak akan dihina dan tersipu-sipu. Engkau akan melupakan ketidaksetiaanmu di waktu muda; tidak mengingat lagi kesepianmu sebagai janda.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Penciptamu seperti suami bagimu, Allah kudus Israel adalah Penyelamatmu. TUHAN Yang Mahakuasa, itulah nama-Nya, Ia Allah penguasa seluruh dunia.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
Israel, engkau seperti seorang istri muda yang sedih karena ditinggalkan suaminya. Tetapi Allah memanggil engkau kembali dan berkata,
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
"Hanya sesaat lamanya Aku meninggalkan engkau; dengan penuh kasih sayang engkau Kuambil kembali.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
Sebentar saja Aku berpaling daripadamu karena kemarahan-Ku yang meluap-luap. Tetapi dengan kasih abadi Aku mengasihani engkau." Demikianlah kata Allah Penyelamatmu.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
"Seperti di masa Nuh Aku berjanji bahwa air bah tak akan lagi menggenangi bumi, begitu juga sekarang Aku berjanji bahwa Aku tak akan marah atau mengancam kamu lagi.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Biarpun gunung-gunung dan bukit-bukit goyah, Aku tak akan berhenti mengasihi engkau. Perjanjian damai-Ku akan Kupegang selalu," kata TUHAN yang mengasihi engkau.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
TUHAN berkata, "Hai Yerusalem, kota yang malang, engkau tak berdaya dan tanpa penghibur. Dasar-dasarmu akan Kuletakkan kembali, dengan batu-batu berharga.
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
Benteng-benteng Kubangun dari batu delima, pintu-pintu gerbangmu dari batu permata, tembok-tembokmu dari ratna mutu manikam.
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Semua pendudukmu menjadi murid-Ku, mereka akan makmur sejahtera.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Engkau dibangun atas dasar keadilan, dijauhkan dari kengerian dan penindasan.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Bila engkau diserbu, bukanlah Aku yang menyuruh, siapa saja yang menyerang engkau akan jatuh.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
Akulah yang menciptakan tukang besi yang mengipas api untuk menempa senjata. Akulah juga yang menjadikan prajurit yang memakai senjata itu untuk membunuh.
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
Tetapi setiap senjata yang ditempa untuk melawan engkau, tak akan berhasil. Dan setiap tuduhan dalam pengadilan akan kaubuktikan salah. Aku akan menghadiahkan kemenangan kepada hamba-hamba-Ku," demikianlah kata TUHAN.

< Ishaya 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark