< Ishaya 54 >
1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
Loue le Seigneur, stérile, qui n’enfantes pas; chante sa louange, et pousse des cris de joie, toi qui n’enfantais pas: parce que les fils de la délaissée seront plus nombreux que les fils de celle qui a un mari, dit le Seigneur.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Elargis l’enceinte de ta tente, et étends les peaux de tes tabernacles; n’épargne rien; allonge tes cordages, et affermis tes pieux.
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Car tu pénétreras à droite et à gauche, et ta race aura des nations pour héritage, et elle habitera des villes auparavant désertes.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
Ne crains pas, parce que tu ne seras pas confondue, et tu ne rougiras pas; car tu n’auras pas de honte, parce que tu oublieras la confusion de ta jeunesse; et de l’opprobre de ta viduité, tu ne te souviendras plus.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Parce que celui qui t’a faite te dominera; le Seigneur des armées est son nom, et ton rédempteur, le saint d’Israël, sera appelé le Dieu de toute la terre.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
Car le Seigneur t’a appelée comme une femme délaissée et affligée d’esprit, et comme une femme répudiée dès sa jeunesse, a dit ton Dieu.
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
Pour un instant je t’ai un peu délaissée, mais dans mes grandes miséricordes je te rassemblerai.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
Dans un moment d’indignation je t’ai caché ma face pendant un peu de temps, mais dans ma miséricorde éternelle, j’ai eu pitié de toi, a dit ton rédempteur le Seigneur.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
C’est ici pour moi comme aux jours de Noé, à qui je jurai que je n’amènerais plus les eaux de Noé sur la terre; ainsi j’ai juré que je ne me mettrai pas en colère contre toi, et que je ne te réprimanderai pas.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Car les montagnes seront ébranlées et les collines frémiront; mais ma miséricorde ne se retirera pas de toi, et mon alliance de paix ne sera pas ébranlée, a dit celui qui a pitié de toi, le Seigneur.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
Tu es pauvre, battue par la tempête, et sans aucune consolation. Voici que moi j’alignerai tes pierres, et tu seras fondée sur des saphirs.
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
Et je ferai tes tours de jaspe, et tes portes en pierres ciselées, et tous tes contours en pierres précieuses;
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Et tous tes fils seront instruits par le Seigneur, et une abondance de paix est réservée à tes fils.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Et tu seras fondée dans la justice; éloigne-toi de la violence, parce que tu n’auras pas à craindre, et de la frayeur, parce qu’elle ne t’approchera pas.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Voici que viendra un habitant qui n’était pas avec moi; que celui qui était étranger autrefois pour toi se joindra à toi.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
Voilà que moi j’ai créé l’ouvrier qui souffle dans le feu des charbons ardents, et en fait sortir un instrument pour son ouvrage, et c’est moi qui ai créé le meurtrier pour détruire.
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
Tout instrument qui a été imaginé contre toi manquera le but; et toute langue qui te résistera dans le jugement, tu la jugeras. C’est là l’héritage des serviteurs du Seigneur, et la justice qu’ils trouvent auprès de moi, dit le Seigneur.