< Ishaya 54 >

1 “Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
Réjouis-toi avec chant de triomphe, stérile [qui] n'enfantais point, [toi qui] ne savais ce que c'est du travail d'enfant, éclate de joie avec chant de triomphe, et t'égaye; car les enfants de celle qui était délaissée, [seront] en plus grand nombre que les enfants de celle qui était mariée, a dit l'Eternel.
2 “Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
Elargis le lieu de ta tente, et qu'on étende les courtines de tes pavillons; n'épargne rien, allonge tes cordages, et fais tenir ferme tes pieux.
3 Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
Car tu te répandras à droite et à gauche, et ta postérité possédera les nations, et rendra habitées les villes désertes.
4 “Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
Ne crains point, car tu ne seras point honteuse, ni confuse, et tu ne rougiras point; mais tu oublieras la honte de ta jeunesse, et tu ne te souviendras plus de l'opprobre de ton veuvage.
5 Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
Car ton mari est celui qui t'a faite; l'Eternel des armées est son Nom; et ton Rédempteur est le Saint d'Israël: il sera appelé le Dieu de toute la terre.
6 Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
Car l'Eternel t'a appelée comme une femme délaissée et travaillée en son esprit, et comme une femme qu'on aurait épousée dans la jeunesse, et qui aurait été répudiée, a dit ton Dieu.
7 “Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
Je t'ai délaissée pour un petit moment; mais je te rassemblerai par de grandes compassions.
8 Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
J'ai caché ma face arrière de toi pour un moment dans le temps de l'indignation; mais j'ai eu compassion de toi par une gratuité éternelle, a dit l'Eternel ton Rédempteur.
9 “A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
Car ceci me sera [comme] les eaux de Noé; c'est que [comme] j'ai juré que les eaux de Noé ne passeront plus sur la terre; ainsi j'ai juré que je ne serai plus indigné contre toi, et que je ne te tancerai plus.
10 Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
Car quand les montagnes se remueraient, et que les coteaux crouleraient, ma gratuité ne se retirera point de toi, et l'alliance de ma paix ne bougera point, a dit l'Eternel, qui a compassion de toi.
11 “Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
O affligée! agitée de la tempête, destituée de consolation, voici, je m'en vais coucher des escarboucles pour tes pierres, et je te fonderai sur des saphirs;
12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
Et je ferai tes fenêtrages d'agates, et tes portes seront de pierres de rubis, et toute ton enceinte de pierres précieuses.
13 Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
Aussi tous tes enfants seront enseignés de l'Eternel, et la paix de tes fils sera abondante.
14 Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
Tu seras affermie en justice, tu seras loin de l'oppression, et tu ne craindras rien; tu seras, dis-je, loin de la frayeur, car elle n'approchera point de toi.
15 In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
Voici, on ne manquera pas de comploter [contre toi], mais ce ne sera pas de par moi; quiconque complotera contre toi, tombera pour l'amour de toi.
16 “Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
Voici, c'est moi qui ai créé le forgeron soufflant le charbon au feu, et formant l'instrument pour son ouvrage; et c'est moi qui ai créé le destructeur pour dissiper.
17 ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.
Nulles armes forgées contre toi ne prospéreront, et tu convaincras de malice toute langue qui se sera élevée contre toi en jugement; c'est là l'héritage des serviteurs de l'Eternel, et leur justice de par moi, dit l'Eternel.

< Ishaya 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark