< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Хто нашій спасе́нній тій звістці повірив, і над ким відкрива́лось раме́но Господнє?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Бо Він виріс перед Ним, мов галу́зка, і мов корінь з сухої землі, — не мав Він прина́ди й не мав пишноти́; і ми Його бачили, та краси́ не було, щоб Його пожада́ти!
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Він пого́рджений був, Його люди покинули, стра́дник, знайо́мий з хоро́бами, і від Якого обличчя ховали, пого́рджений, і ми не цінува́ли Його.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Направду ж Він не́мочі наші узяв і наші болі поніс, а ми уважали Його за пора́неного, ніби Бог Його вдарив поразами й мучив.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
А Він був ране́ний за наші гріхи, за наші прови́ни Він му́чений був, — кара на Ньому була за наш мир, Його ж ра́нами нас уздоро́влено!
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Усі ми блуди́ли, немов ті овечки, розпоро́шились кожен на власну дорогу, — і на Нього Господь покла́в гріх усіх нас!
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Він гно́блений був та пони́жуваний, але уст Своїх не відкрива́в. Як ягня був прова́джений Він на зако́лення, й як овечка перед стрижія́ми своїми мовчи́ть, так і Він не відкрива́в Своїх уст.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Від у́тиску й су́ду Він за́браний був, і хто збагне́ Його рід? Бо з кра́ю живих Він віді́рваний був, за прови́ни Мого наро́ду на смерть Його да́но.
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
Із злочинцями ви́значили Йому гро́ба Його, та Його поховали в багатого, хоч провини Він не учини́в, і не було в Його у́стах ома́ни.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Та зво́лив Господь, щоб поби́ти Його, щоб му́ки завда́но Йому. Якщо ж душу Свою покладе́ Він як жертву за гріх, то побачить насі́ння, і житиме довгії дні, і за́мір Господній рукою Його буде мати пово́дження!
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Він через му́ки Своєї душі буде бачити плід, та й наси́титься. Справедливий, Мій Слуга, оправдає пізна́нням Своїм багатьох, і їхні гріхи́ понесе́.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
Тому то дам у́діл Йому між великими, і з поту́жними буде ділити здобич за те, що на смерть віддав душу Свою, і з злочинцями був порахо́ваний, хоч гріх багатьо́х Сам носи́в і заступа́всь за злочинців!

< Ishaya 53 >