< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Ngubani olikholiweyo ilizwi lethu, njalo amandla kaThixo abonakaliswe kubani na?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Wakhula phambi kwakhe njengehlumela, lanjengempande emhlabathini owomileyo. Wayengelabuhle lobukhosi ukuba asikhange, kungelalutho esimeni sakhe olungenza simfune.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Weyiswa njalo waliwa ngabantu, umuntu wezinsizi, njalo ekujayele ukuhlupheka. Lowo abantu abangafuniyo ukukhangelana laye weyiswa, asimhloniphanga.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Ngempela wathatha inhlungu zethu wathwala insizi zethu, kodwa thina sathi utshaywe nguNkulunkulu, ebethwe nguye, njalo uhlutshiwe.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
Kodwa wagwazwa ngenxa yezono zethu, wachobozwa ngenxa yokona kwethu, ukuhlutshwa kwakhe kwasilethela ukuthula, njalo sasiliswa ngamanxeba akhe.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Thina sonke silahlekile njengezimvu, munye ngamunye wethu uphambukele endleleni yakhe; njalo uThixo ubeke phezu kwakhe ukona kwethu sonke.
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Wancindezelwa wahlutshwa, kodwa kawuvulanga umlomo wakhe; wakhokhelwa ukuyabulawa njengewundlu, njalo njengemvu ithule phambi komgundi wayo, laye kawuvulanga umlomo wakhe.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Ngokuncindezelwa langokwahlulela wathathwa. Ngubani ongakhuluma ngesizukulwane sakhe na? Ngoba wasuswa elizweni labaphilayo; watshaywa ngenxa yeziphambeko zabantu bami.
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
Wabelwa ingcwaba kanye lababi, kanye labanothileyo ekufeni kwakhe, lanxa kungeladlakela alwenzayo njalo kungekho inkohliso emlonyeni wakhe.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Ikanti kwakuyintando kaThixo ukumchoboza lokumenza ahlupheke, njalo lanxa uThixo esenza ukuphila kwakhe umnikelo wecala, uzabona inzalo yakhe, andise insuku zokuphila kwakhe, lentando kaThixo izaphumelela ngaye.
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Emva kokuhlupheka komoya wakhe, uzabona ukukhanya kokuphila asuthiseke; ngokwazi kwayo inceku yami elungileyo izalungisa abanengi, ithwale izono zabo.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
Ngakho-ke ngizamnika isabelo phakathi kwabakhulu, njalo uzakwabelana impango labalamandla ngoba wanikela ukuphila kwakhe ekufeni, wabalwa ndawonye lezoni; ngoba wathwala izono zabanengi, wancengela izoni.

< Ishaya 53 >