< Ishaya 53 >
1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Who hath believed our report, And to whom hath the arm of Jehovah been revealed?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
For He grew up before him like a tender plant, Like a sucker from a dry soil; He had no form, nor comeliness, that we should look upon him, Nor beauty, that we should take pleasure in him.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
He was despised, and forsaken of men, A man of sorrows, and acquainted with disease; As one from whom men hide their faces, He was despised, and we esteemed him not.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
But he bore our diseases, And carried our pains, And we esteemed him stricken from above, Smitten of God, and afflicted.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
But he was wounded for our transgressions; He was bruised for our iniquities; For our peace was the chastisement upon him, And by his stripes are we healed.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
All we, like sheep, were going astray; We turned every one to his own way, And Jehovah laid upon him the iniquity of us all.
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
He was oppressed, that was already afflicted. Yet he opened not his mouth; As a lamb that is led to the slaughter, And as a sheep before her shearers is dumb, He opened not his mouth.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
By oppression and punishment he was taken away, And who in his generation would consider That he was cut off from the land of the living, That for the transgression of my people he was smitten?
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
His grave was appointed with the wicked, And with the rich man was his sepulchre, Although he had done no injustice, And there was no deceit in his mouth.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
It pleased Jehovah severely to bruise him; But when he hath made his life a sacrifice for sin, He shall see posterity; he shall prolong his days, And the pleasure of Jehovah shall prosper in his hand.
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Free from his sorrows, he shall see and be satisfied; By his knowledge shall my righteous servant lead many to righteousness, And he shall bear their iniquities.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
Therefore will I give him his portion with the mighty, And with heroes shall he divide the spoil, Because he poured out his soul unto death, And was numbered with transgressors; Because he bore the sin of many, And made intercession for transgressors.