< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Hvo troede det, vi have hørt? og for hvem er Herrens Arm aabenbaret?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Thi han skød frem som en Kvist for hans Ansigt og som et Rodskud af tør Jord, han havde ingen Skikkelse eller Herlighed; og vi saa ham, men der var ikke Anseelse, at vi kunde have Lyst til ham.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Han var foragtet og ikke at regne iblandt Mænd, en Mand fuld af Pine og forsøgt i Sygdom; og som en, for hvem man skjuler Ansigtet, foragtet, og vi agtede ham for intet.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Visselig, han har taget vore Sygdomme paa sig og baaret vore Smerter; men vi agtede ham for plaget, slagen af Gud og gjort elendig.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
Men han er saaret for vore Overtrædelser og knust for vore Misgerninger; Straffen er lagt paa ham, at vi skulle have Fred, og vi have faaet Lægedom ved hans Saar.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Vi fore alle vild som Faar, vi vendte os hver sin Vej; men Herren lod al vor Misgerning komme over ham.
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Han blev trængt, og han blev gjort elendig, men han oplod ikke sin Mund, som et Lam, der føres hen at slagtes, og som et Faar, der er stumt over for dem, som klippe det; og han oplod ikke sin Mund.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Fra Trængsel og fra Dom er han borttagen, og hvo kan tale om hans Slægt? thi han er bortreven fra de levendes Land, han havde Plage for mit Folks Overtrædelses Skyld.
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
Og man gav ham hans Grav hos de ugudelige, og hos den rige i hans Død, uagtet han ikke havde gjort Uret, og der ikke var Svig i hans Mund.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Men Herren havde Behag i at knuse ham med Sygdom; naar hans Sjæl har fuldbragt et Skyldoffer, skal han se Sæd og forlænge sine Dage; og Herrens Villie skal lykkes ved hans Haand.
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Fordi hans Sjæl har haft Møje, skal han se det, hvorved han skal mættes; naar han kendes, skal min retfærdige Tjener retfærdiggøre de mange; og han skal bære deres Misgerninger.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
Derfor vil jeg give ham Del i de mange, og han skal dele de stærke som et Bytte, fordi han udtømte sin Sjæl til Døden og blev regnet iblandt Overtrædere; ja han har baaret manges Synd, og han skal bede for Overtrædere.

< Ishaya 53 >