< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Kdo uvěřil kázaní našemu? A rámě Hospodinovo komu jest zjeveno?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Nebo před ním vyrostl jako proutek, a jako kořen z země vyprahlé, nemaje podoby ani krásy. Viděliť jsme jej, ale nic nebylo viděti toho, proč bychom ho žádostivi byli.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Nejpohrdanější zajisté a nejopovrženější byl z lidí, muž bolestí, a kterýž zkusil nemocí, a jako ukrývající tvář svou; nejpohrdanější, pročež jsme ho za nic nevážili.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Ještotě on nemoci naše vzal, a bolesti naše vlastní on nesl, my však domnívali jsme se, že jest raněn, a ubit od Boha, i strápen.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
On pak raněn jest pro přestoupení naše, potřín pro nepravosti naše; kázeň pokoje našeho na něj vzložena, a zsinalostí jeho lékařství nám způsobeno.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Všickni my jako ovce zbloudili jsme, jeden každý na cestu svou obrátili jsme se, a Hospodin uvalil na něj nepravosti všech nás.
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Pokutován jest i strápen, však neotevřel úst svých. Jako beránek k zabití veden byl, a jako ovce před těmi, kdož ji střihou, oněměl, aniž otevřel úst svých.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Z úzkosti a z soudu vyňat jest, a protož rod jeho kdo vypraví, ačkoli vyťat jest z země živých, a zraněn pro přestoupení lidu mého?
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
Kterýžto vydal bezbožným hrob jeho, a bohatému, aby byl usmrcen, ješto však nepravosti neučinil, aniž jest nalezena lest v ústech jeho.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Taktě se líbilo Hospodinu jej stírati, a nemocí trápiti, aby polože duši svou v oběť za hřích, viděl símě své, byl dlouhověký, a to, což se líbí Hospodinu, skrze něho šťastně konáno bylo.
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Z práce duše své uzří užitek, jímž nasycen bude. Známostí svou ospravedlní spravedlivý služebník můj mnohé; nebo nepravosti jejich on sám ponese.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
A protož dám jemu díl pro mnohé, aby s nesčíslnými dělil se o kořist, proto že vylil na smrt duši svou, a s přestupníky počten jest. Onť sám nesl hřích mnohých, a přestupníků zástupcím byl.

< Ishaya 53 >