< Ishaya 52 >

1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Uyan, ey Siyon, uyan, kudretini kuşan. Ey Yeruşalim, kutsal kent, güzel giysilerini giy. Çünkü sünnetsizlerle murdarlar Kapılarından asla içeri girmeyecek artık.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Üzerindeki tozu silk! Kalk, ey Yeruşalim, tahtına otur, Boynundaki zinciri çöz, Ey Siyon, tutsak kız.
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
RAB diyor ki, “Karşılıksız satılmıştınız, Parasız kurtulacaksınız.”
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
Egemen RAB diyor ki, “Halkım gurbette yaşamak için önce Mısır'a inmişti. Şimdi de Asurlular onları ezdi.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Halkım boş yere alınıp götürüldü, Benim burayla ne ilgim kaldı?” diyor RAB, “Yöneticileri feryat ediyor, Adıma günboyu sövülüyor” diyor RAB.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
“Bundan ötürü halkım adımı bilecek, O gün, ‘İşte ben’ diyenin ben olduğumu anlayacak.”
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
Dağları aşıp gelen müjdecinin ayakları ne güzeldir! O müjdeci ki, esenlik duyuruyor. İyilik müjdesi getiriyor, kurtuluş haberi veriyor. Siyon halkına, “Tanrınız egemenlik sürüyor!” diye ilan ediyor.
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
Dinleyin! Bekçileriniz seslerini yükseltiyor, Hep birlikte sevinçle haykırıyorlar. Çünkü RAB'bin Siyon'a dönüşünü gözleriyle görmekteler!
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Ey Yeruşalim yıkıntıları, Hep birlikte sevinçle haykırıp bağırın! Çünkü RAB halkını avuttu, Yeruşalim'i kurtardı.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
Bütün ulusların gözü önünde Kutsal kolunu sıvadı, Dünyanın dört bucağı Tanrımız'ın kurtarışını görecek.
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Çekilin, çekilin, oradan çıkın, Murdara dokunmayın. Oradan çıkıp temizlenin, Ey RAB'be tapınma araçlarını taşıyan sizler!
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
Aceleyle çıkmayacak, Kaçıp gitmeyeceksiniz; Çünkü RAB önünüzden gidecek, İsrail'in Tanrısı artçınız olacak.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Bakın, kulum başarılı olacak; Üstün olacak, el üstünde tutulup alabildiğine yüceltilecek.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Birçokları onun karşısında dehşete düşüyor; Biçimi, görünüşü öyle bozuldu ki, İnsana benzer yanı kalmadı;
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
Pek çok ulus ona şaşacak, Onun önünde kralların ağızları kapanacak. Çünkü kendilerine anlatılmamış olanı görecek, Duymadıklarını anlayacaklar.

< Ishaya 52 >