< Ishaya 52 >

1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Vuka, vuka, wembathe amandla akho, Ziyoni! Yembatha izembatho zakho ezinhle, Jerusalema, muzi ongcwele! Ngoba kakusayikungena kuwe futhi ongasokanga longcolileyo.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Zithintithe usuke othulini, sukuma, uhlale phansi, Jerusalema! Zikhululekuzibopho zentamo yakho, ndodakazi ethunjiweyo yeZiyoni!
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
Ngoba itsho njalo iNkosi: Lathengiswa ngeze; njalo lizahlengwa ngaphandle kwemali.
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
Ngoba itsho njalo iNkosi uJehova: Abantu bami behlela eGibhithe esikhathini sendulo ukuhlala njengabezizwe khona, njalo iAsiriya yabacindezela ngaphandle kwesizatho.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Khathesi-ke, ngilani lapha, itsho iNkosi, ukuthi abantu bami bathethwe ngeze? Labo abababusayo babenza baqhinqe isililo, itsho iNkosi, lebizo lami liqhubeka lihlanjazwa lonke usuku.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
Ngakho abantu bami bazalazi ibizo lami; ngakho ngalolosuku bazakwazi ukuthi yimi engikhulumayo; khangela, yimi.
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
Zinhle kangakanani phezu kwezintaba inyawo zalowo oletha izindaba ezinhle, omemezela ukuthula, oletha indaba ezinhle zokulunga, ozwakalisa usindiso, othi kuyo iZiyoni: UNkulunkulu wakho uyabusa.
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
Ilizwi labalindi bakho! Bazaphakamisa ilizwi, bahlabele kakhulu kanyekanye, ngoba bazabona ilihlo ngelihlo, lapho iNkosi izabuyisa iZiyoni.
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Qhamukani ngentokozo, lihlabelele kanyekanye, lina manxiwa eJerusalema, ngoba iNkosi isibaduduzile abantu bayo, iyihlengile iJerusalema.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
INkosi yembule ingalo yayo engcwele emehlweni azo zonke izizwe, njalo imikhawulo yonke yomhlaba izabona usindiso lukaNkulunkulu wethu.
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Sukani, sukani, liphume lapha, lingathinti okungcolileyo, phumani phakathi kwayo, banini ngabahlambulukileyo, lina elithwala izitsha zeNkosi.
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
Ngoba kaliyikuphuma ngokuphangisa, kumbe lihambe ngokubaleka, ngoba iNkosi izahamba phambi kwenu, loNkulunkulu kaIsrayeli uzakuba ngumvikeli wenu ngasemuva.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Khangela, inceku yami izakwenza ngenhlakanipho, iphakeme njalo iphakanyisiwe, iphakeme kakhulu.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Njengoba abanengi babethithibele ngawe; ukukhangeleka kwayo kwakonakele kangaka, okwedlula loba nguwuphi, lesimo sayo okwedlula amadodana abantu.
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
Ngokunjalo izafafaza izizwe ezinengi; amakhosi azayivalela umlomo wawo; ngoba lokho abangakulandiselwanga bazakubona, lalokho abangakuzwanga bazakuqedisisa.

< Ishaya 52 >