< Ishaya 52 >

1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Vuka, vuka, wena Ziyoni, uzembese ngamandla! Gqoka izigqoko zakho zenkazimulo, wena Jerusalema, muzi ongcwele. Ongasokanga longcolileyo akayikungena kuwe futhi.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Thintitha uthuli lwakho; sukuma, uhlale ebukhosini, wena Jerusalema. Zikhulule izibopho ezisentanyeni yakho, wena Ndodakazi ethunjiweyo yaseZiyoni.
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
Ngoba nanku okutshiwo nguThixo: “Lathengiswa ngeze, njalo lizahlengwa kungekho mali.”
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
Ngoba nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: “Ekuqaleni abantu bami baya eGibhithe besiyahlala khona; muva i-Asiriya yabancindezela.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Khathesi kuyini engilakho lapha?” kubuza uThixo. “Ngoba abantu bami bathunjwa kungekho sizatho, njalo labo abababusayo bayakloloda,” kutsho uThixo. “Ilanga lonke ibizo lami lihlanjazwa kokuphela.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
Ngakho-ke abantu bami bazalazi ibizo lami, ngakho-ke ngalolosuku bazakwazi ukuthi yimi engamemezela lokho ngaphambilini. Yebo, yimi.”
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
Yeka ubuhle phezu kwezintaba, bezinyawo zalabo abaletha izindaba ezinhle, abamemezela ukuthula, abaletha izindaba ezinhle, abamemezela insindiso, abathi kulo iZiyoni, “UNkulunkulu wakho uyabusa!”
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
Lalela! Abalindi bakho baphakamisa amazwi abo, bonke bahlaba umkhosi ngokuthokoza. Lapho uThixo ebuyela eZiyoni bazayibona iZiyoni ngamehlo abo.
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Hlokomani ndawonye ngezingoma zokuthokoza, lina manxiwa aseJerusalema, ngoba uThixo usebaduduzile abantu bakhe, uselihlengile iJerusalema.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
UThixo uzaveza ingalo yakhe engcwele phambi kwezizwe zonke, njalo yonke imikhawulo yomhlaba izabona insindiso kaNkulunkulu wethu.
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Sukani, sukani, phumani lapho! Lingathinti lutho olungcolileyo! Phumani kulo libe ngabahlambulukileyo, lina eliphatha izitsha zikaThixo.
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
Kodwa kaliyikusuka ngokuphangisa, kumbe libaleka; ngoba uThixo uzahamba phambi kwenu, uNkulunkulu ka-Israyeli uzakuba ngumvikeli wenu emva kwenu.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Khangelani, inceku yami izakwenza ngokuhlakanipha, izaphakanyiswa ikhwezwe, iphiwe lodumo olukhulu.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Njengoba babebanengi abanengwayo yiyo, ubuso bayo babulimele okudlula okwabantu bonke, lesimo sayo sonakele singase njengesomuntu,
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
ngakho-ke izachela izizwe ezinengi, amakhosi azavala imilomo yawo ngenxa yayo. Ngoba lokho abangakutshelwanga bazakubona, labangakuzwanga, bazakuqedisisa.

< Ishaya 52 >