< Ishaya 52 >
1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Lève-toi, lève-toi, revêts-toi de ta force, Sion; revêts-toi des vêtements de ta gloire, Jérusalem, cité du saint; parce qu’il n’y aura plus à l’avenir d’incirconcis qui passera au travers de toi, ni d’impur.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Sors de la poussière, lève-toi, assieds-toi, Jérusalem; romps les fers de ton cou, captive fille de Sion.
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
Parce que voici ce que dit le Seigneur: Pour rien vous avez été vendus, et sans argent vous serez rachetés.
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu: Mon peuple descendit en Egypte, dans le principe, pour y être colon; et Assur, sans aucun sujet, l’a traité avec violence.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Et maintenant qu’ai-je ici à faire, dit le Seigneur, puisque mon peuple a été enlevé sans motif? Ses dominateurs agissent iniquement, dit le Seigneur, et sans cesse tout le jour mon nom est blasphémé.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
À cause de cela mon peuple connaîtra mon nom en ce jour-là; il saura que moi-même qui parlais autrefois, me voici présent.
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
Qu’ils sont beaux sur les montagnes, les pieds de celui qui annonce et qui prêche la paix; qui annonce le bonheur, qui prêche le salut, qui dit à Sion: il régnera, ton Dieu!
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
La voix de tes sentinelles; elles ont élevé la voix, elles chanteront ensemble des louanges; parce qu’oeil à œil elles verront, lorsque le Seigneur convertira Sion.
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Réjouissez-vous et chantez des louanges ensemble, déserts de Jérusalem; parce que le Seigneur a consolé son peuple, qu’il a racheté Jérusalem.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
Le Seigneur a préparé son bras saint aux yeux de toutes les nations; et ils verront tous les confins de la terre, le salut de notre Dieu.
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Retirez-vous, retirez-vous, sortez de là, ne touchez rien d’impur; sortez du milieu d’elle, purifiez-vous, vous qui portez les vases du Seigneur.
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
Parce que vous ne sortirez point en tumulte, et vous ne vous précipiterez point dans votre fuite; car le Seigneur vous précédera, et le Dieu d’Israël vous rassemblera.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Voici que mon serviteur aura l’intelligence, il sera exalté, élevé et glorieux.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Comme beaucoup ont été frappés de stupeur à ton sujet, ainsi sera sans gloire son aspect parmi les hommes, et sa forme parmi les fils des hommes.
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
C’est lui qui aspergera beaucoup de nations; devant lui, des rois fermeront leur bouche; parce que ceux à qui il n’avait pas été parlé de lui, l’ont vu; et ceux qui n’en avaient pas entendu parler, l’ont contemplé.