< Ishaya 52 >
1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Réveille-toi, réveille-toi, revêts ta gloire, ô Sion! Revêts ton vêtement de parure, Jérusalem, ville sainte! Car il n'entrera plus chez toi d'incirconcis ni d'impur.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Secoue ta poussière, lève-toi, Jérusalem captive; détache les liens de ton cou, fille de Sion prisonnière!
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
Car ainsi a dit l'Éternel: Vous avez été vendus pour rien; vous serez aussi rachetés sans argent.
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
Car ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Mon peuple descendit jadis en Égypte pour y habiter; mais Assur l'a opprimé sans sujet.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Et maintenant qu'ai-je à faire ici, dit l'Éternel, quand mon peuple a été enlevé pour rien? Ceux qui dominent sur lui poussent des cris, dit l'Éternel, et chaque jour, mon nom est continuellement outragé.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
C'est pourquoi mon peuple connaîtra mon nom; c'est pourquoi il saura, en ce jour, que c'est moi qui dis: Me voici!
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
Qu'ils sont beaux sur les montagnes, les pieds de celui qui apporte de bonnes nouvelles, qui publie la paix, qui apporte un bon message, qui publie le salut, qui dit à Sion: Ton Dieu règne!
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
On entend la voix de tes sentinelles: elles élèvent la voix; elles poussent ensemble des cris de joie; car elles voient de leurs yeux que l'Éternel ramène Sion.
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Éclatez ensemble en cris de joie, ruines de Jérusalem! Car l'Éternel a consolé son peuple, il a racheté Jérusalem.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
L'Éternel a découvert le bras de sa sainteté, devant les yeux de toutes les nations; tous les bouts de la terre verront le salut de notre Dieu!
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Retirez-vous, retirez-vous, sortez de là! Ne touchez à rien d'impur, sortez du milieu d'elle; purifiez-vous, vous qui portez les vases de l'Éternel!
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
Car vous ne sortirez pas à la hâte, et vous ne marcherez pas en fuyant; mais l'Éternel marche devant vous, et votre arrière garde est le Dieu d'Israël.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Voici, mon serviteur prospérera; il montera, il s'élèvera, il grandira puissamment.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Comme plusieurs ont été étonnés à cause de lui, tant son visage était défait et méconnaissable, tant son aspect différait de celui des hommes; ainsi il remplira de joie plusieurs nations;
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
Les rois fermeront la bouche devant lui; car ils verront ce qui ne leur avait pas été raconté, ils apprendront ce qu'ils n'avaient point entendu.