< Ishaya 52 >

1 Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
Awake, awake, put on thy strength, O Zion. Put on thy beautiful garments, O Jerusalem, the holy city. For henceforth there shall no more come into thee the uncircumcised and the unclean.
2 Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
Shake thyself from the dust. Arise, sit up, O Jerusalem. Loose thyself from the bonds of thy neck, O captive daughter of Zion.
3 Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
For thus says Jehovah: Ye were sold for nothing, and ye shall be redeemed without money.
4 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
For thus says the lord Jehovah, My people went down at the first into Egypt to sojourn there. And the Assyrian has oppressed them without cause.
5 “Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
Now therefore, what do I do here, says Jehovah, seeing that my people are taken away for nothing? Those who rule over them howl, says Jehovah, and because of you my name is continually blasphemed among the Gentiles.
6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
Therefore my people shall know my name. Therefore they shall know in that day that I am he who speaks, Behold, it is I.
7 Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
How beautiful upon the mountains are the feet of him who brings good news, who publishes peace, who brings good news of good, who publishes salvation, who says to Zion, Thy God reigns!
8 Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
The voice of thy watchmen! They lift up the voice; they sing together. For they shall see eye to eye, when Jehovah returns to Zion.
9 Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
Break forth into joy, sing together, ye waste places of Jerusalem, for Jehovah has comforted his people. He has redeemed Jerusalem.
10 Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
Jehovah has made bare his holy arm in the eyes of all the nations, and all the ends of the earth have seen the salvation of our God.
11 Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
Depart ye, depart ye, go ye out from there. Touch no unclean thing. Go ye out of the midst of her. Cleanse yourselves, ye who bear the vessels of Jehovah.
12 Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
For ye shall not go out in haste, nor shall ye go by flight. For Jehovah will go before you, and the God of Israel will be your rearward.
13 Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
Behold, my servant shall deal wisely. He shall be exalted and lifted up, and shall be very high.
14 Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
Just as many were astonished at thee (his visage was so marred, more than any man, and his form more than the sons of men),
15 haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.
so shall he sprinkle many nations. Kings shall shut their mouths at him. For that which had not been told them they shall see, and that which they had not heard they shall understand.

< Ishaya 52 >