< Ishaya 51 >

1 “Ku kasa kunne gare ni, ku da kuna neman adalci kuke kuma neman Ubangiji. Dubi dutse daga inda aka yanke ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka fafe ku;
“Listen to Me, you pursuing righteousness, Seeking YHWH, Look attentively to the rock—you have been hewn, And to the hole of the pit—you have been dug.
2 dubi Ibrahim, mahaifinku, da Saratu, wadda ta haife ku. Sa’ad da na kira shi kaɗai ne, na kuma albarkace shi na kuma mai da shi da yawa.
Look attentively to your father Abraham, And to Sarah—she brings you forth, For—one—I have called him, And I bless him, and multiply him.”
3 Tabbatacce Ubangiji zai ta’azantar da Sihiyona zai kuma duba da tausayi a kan dukan kufanta; zai sa hamadanta ta zama kamar Eden, ƙeƙasasshiyar ƙasarta kamar lambun Ubangiji. Za a sami farin ciki da murna a cikinta, godiya da ƙarar rerawa.
For YHWH has comforted Zion, He has comforted all her ruins, And He sets her wilderness as Eden, And her desert as a garden of YHWH, Joy, indeed, gladness is found in her, Confession, and the voice of song.
4 “Ku kasa kunne gare ni, mutanena; ku ji ni, al’ummata. Doka za tă fito daga gare ni; shari’ata za tă zama haske ga al’ummai.
“Attend to Me, O My people, And, O My nation, give ear to Me. For a law goes out from Me, And My judgment to the light, I cause peoples to rest.
5 Adalcina na zuwa da sauri, cetona yana a kan hanya, hannuna kuma zai kawo adalci ga al’ummai. Tsibirai za su dube ni su kuma jira da sa zuciya don hannuna.
My righteousness [is] near, My salvation has gone out, And My arms judge peoples, Islands wait on Me, Indeed, on My arm they wait with hope.
6 Ku daga idanunku zuwa sammai ku dubi duniya a ƙasa; sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za tă shuɗe kamar riga mazaunanta kuma su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai dawwama har abada, adalcina ba zai taɓa kāsa ba.
Lift up your eyes to the heavens, And look attentively to the earth beneath, For the heavens have vanished as smoke, And the earth wears out as a garment, And its inhabitants die as gnats, And My salvation is for all time, And My righteousness is not broken.
7 “Ku ji ni, ku da kuka san abin da yake daidai, ku mutanen da kuke da dokata a zukatanku. Kada ku ji tsoron ba’ar da mutane suke yi ko ku firgita saboda zargin da suke yi.
Listen to Me, you who know righteousness, A people in whose heart [is] My law, Do not fear the reproach of men, And do not be frightened of their reviling,
8 Gama asu za su cinye su kamar riga; tsutsotsi za su cinye su kamar ulu. Amma adalcina zai dawwama har abada, cetona har dukan zamanai.”
For a moth eats them as a garment, And a worm eats them as wool, And My righteousness is for all time, And My salvation from generation to generation.”
9 Ka tashi, ka tashi! Ka yafa wa kanka ƙarfi, Ya hannun Ubangiji; ka farka, kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a zamanai na dā. Ba kai ba ne wanda ya yayyanka Rahab gunduwa-gunduwa, wanda ya soki dodon ruwan nan?
Awake, awake, put on strength, O arm of YHWH, Awake, as [in] days of old, generations of the ages, Are You not it that is hewing down Rahab, Piercing a dragon?
10 Ba kai ba ne ka busar da teku, ka busar da ruwan zurfafa masu girma, wanda ya yi hanya a cikin zurfafan teku saboda fansassu su ƙetare?
Are You not it that is drying up a sea, Waters of a great deep? That has made deep places of a sea A way for the passing of the redeemed?
11 Waɗanda Ubangiji ya fansar za su dawo. Za su shiga Sihiyona da waƙoƙi; madawwamin farin ciki zai rufe kansu da rawani. Murna da farin ciki zai cika su, baƙin ciki da nishi zai ɓace.
And the ransomed of YHWH return, And they have come to Zion with singing, And continuous joy [is] on their head, They attain gladness and joy, Sorrow and sighing have fled away,
12 “Ni kaɗai ne na ta’azantar da ku. Wane ne ku da kuke tsoron mutane masu mutuwa,’ya’yan mutane waɗanda suke ciyawa ne kawai,
“I [am] He who comforts you, Who [are] you—and you are afraid of man? He dies! And of the son of man—he is made [like] grass!
13 har da kuka manta da Ubangiji Mahaliccinku, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya, har kuna zama da tsoro kowace rana saboda fushin masu zalunci, waɗanda sun ƙudura sai sun hallaka? Gama ina fushin mai zalunci?
And you forget YHWH your Maker, Who is stretching out the heavens, and founding earth, And you continually fear all the day, Because of the fury of the oppressor, As he has prepared to destroy. And where [is] the fury of the oppressor?
14 Ba da daɗewa za a’yantar da’yan kurkuku; ba za su mutu a kurkuku ba, ba kuwa za su rasa abinci ba.
A wanderer has hurried to be loosed, And he does not die in the pit, And his bread is not lacking.
15 Gama ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya dama teku domin raƙumansa su yi ruri, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
And I [am] your God YHWH, Quieting the sea when its billows roar, YHWH of Hosts [is] His Name.
16 Na sa maganata a bakinka na kuma rufe ka da inuwar hannuna, Na shimfiɗa sammai, na kafa harsashen duniya, na kuma ce wa Sihiyona, ‘Ku mutanena ne.’”
And I put My words in your mouth, And have covered you with the shadow of My hand, To plant the heavens, and to found earth, And to say to Zion, You [are] My people.”
17 Ki farka, ki farka! Ki tashi, ya Urushalima, ke da kika sha daga hannun Ubangiji kwaf na fushinsa, ke da kika shanye har ƙasar kwaf kwaf da ya sa mutane suna tangaɗi.
Stir yourself, stir yourself, rise, Jerusalem, You who have drunk from the hand of YHWH The cup of His fury, The goblet, the cup of trembling, you have drunk, You have wrung out.
18 Cikin dukan’ya’yan da ta haifa; cikin dukan’ya’yan da ta yi reno babu wani da zai kama hannunta.
There is not a leader to her Out of all the sons she has borne, And there is none laying hold on her hand Out of all the sons she has nourished.
19 Waɗannan masifu riɓi biyu sun auko miki, wa zai ta’azantar da ke? Lalaci da hallaka, yunwa da takobi, wa zai ƙarfafa ki?
These two are meeting you, Who is moved for you? Spoiling and destruction, famine and sword! By whom do I comfort you?
20 ’Ya’yanki sun sume; sun kwanta kusurwar kowane titi, kamar barewar da aka kama da tarko. Sun cika da fushin Ubangiji da kuma tsawatawar Allahnki.
Your sons have been wrapped up, they have lain down, At the head of all out places, as an antelope [in] a dragnet, They are full of the fury of YHWH, The rebuke of Your God.
21 Saboda haka ki ji wannan, ke mai wahala, wadda ta bugu, amma ba da ruwan inabi.
Therefore, please hear this, O afflicted and drunken one, and not with wine,
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Allahnki, wanda ya kāre mutanensa, “Duba, na ƙwace daga hannunki kwaf da ya sa ki tangaɗi; daga wannan kwaf, kwaf na fushina, ba za ki ƙara sha ba.
Thus said your Lord YHWH, and your God, He pleads [for] His people: “Behold, I have taken the cup of trembling out of your hand, The goblet, the cup of My fury, You do not add to drink it anymore.
23 Zan sa shi a hannuwan masu gwada miki azaba, waɗanda suke ce miki, ‘Fāɗi rubda ciki don mu iya taka a kanki.’ Kika kuma mai da bayanki kamar ƙasa, kamar titin da ake takawa a kai.”
And I have put it into the hand of those afflicting you, Who have said to your soul, Bow down, and we pass over, And you make your body as the earth, And as the street to those passing by!”

< Ishaya 51 >