< Ishaya 51 >
1 “Ku kasa kunne gare ni, ku da kuna neman adalci kuke kuma neman Ubangiji. Dubi dutse daga inda aka yanke ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka fafe ku;
Hearken to me, ye that pursue righteousness, that seek the Lord: look unto the rock whence ye were hewn, and to the hole of the pit whence ye were dug up.
2 dubi Ibrahim, mahaifinku, da Saratu, wadda ta haife ku. Sa’ad da na kira shi kaɗai ne, na kuma albarkace shi na kuma mai da shi da yawa.
Look unto Abraham your father, and unto Sarah that bore you; for he was one when I called him, and I blessed him, and I increased him.
3 Tabbatacce Ubangiji zai ta’azantar da Sihiyona zai kuma duba da tausayi a kan dukan kufanta; zai sa hamadanta ta zama kamar Eden, ƙeƙasasshiyar ƙasarta kamar lambun Ubangiji. Za a sami farin ciki da murna a cikinta, godiya da ƙarar rerawa.
Yea, the Lord hath comforted Zion; he hath comforted all her ruins; and he hath made her wilderness like Eden, and her desert like the garden of the Lord: gladness and joy shall be found therein, thanksgiving, and the voice of song.
4 “Ku kasa kunne gare ni, mutanena; ku ji ni, al’ummata. Doka za tă fito daga gare ni; shari’ata za tă zama haske ga al’ummai.
Listen unto me, my people; and O my nation, give ear unto me; for a law shall proceed from me, and my justice will I establish as a light of the people.
5 Adalcina na zuwa da sauri, cetona yana a kan hanya, hannuna kuma zai kawo adalci ga al’ummai. Tsibirai za su dube ni su kuma jira da sa zuciya don hannuna.
My righteousness is near; my salvation goeth forth, and my arms shall judge the people: on me the isles shall wait, and for my arm shall they hope.
6 Ku daga idanunku zuwa sammai ku dubi duniya a ƙasa; sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za tă shuɗe kamar riga mazaunanta kuma su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai dawwama har abada, adalcina ba zai taɓa kāsa ba.
Lift up your eyes to the heavens, and look upon the earth beneath; for the heavens shall vanish away like smoke, and the earth shall wear out like a garment, and they that dwell thereon shall die in like manner; but my salvation shall exist for ever, and my righteousness shall not be delayed.
7 “Ku ji ni, ku da kuka san abin da yake daidai, ku mutanen da kuke da dokata a zukatanku. Kada ku ji tsoron ba’ar da mutane suke yi ko ku firgita saboda zargin da suke yi.
Hearken unto me, ye that know righteousness, O people in whose heart my law is: ye must not fear the reproach of men, and of their revilings shall ye not be in dread.
8 Gama asu za su cinye su kamar riga; tsutsotsi za su cinye su kamar ulu. Amma adalcina zai dawwama har abada, cetona har dukan zamanai.”
For like a garment shall the moth eat them up, and like wool shall the worm eat them; but my righteousness shall exist for ever, and my salvation from generation to generation.
9 Ka tashi, ka tashi! Ka yafa wa kanka ƙarfi, Ya hannun Ubangiji; ka farka, kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a zamanai na dā. Ba kai ba ne wanda ya yayyanka Rahab gunduwa-gunduwa, wanda ya soki dodon ruwan nan?
Awake, awake, put on strength, O arm of the Lord: awake, as in the ancient days, in the generations of olden times. Art thou not it that struck down Rahab, that pierced the crocodile?
10 Ba kai ba ne ka busar da teku, ka busar da ruwan zurfafa masu girma, wanda ya yi hanya a cikin zurfafan teku saboda fansassu su ƙetare?
Art thou not it that dried up the sea, the waters of the great deep; that rendered the depths of the sea a road for the redeemed to pass through?
11 Waɗanda Ubangiji ya fansar za su dawo. Za su shiga Sihiyona da waƙoƙi; madawwamin farin ciki zai rufe kansu da rawani. Murna da farin ciki zai cika su, baƙin ciki da nishi zai ɓace.
And [so] shall the ransomed of the Lord return, and come to Zion with song, with everlasting joy upon their head; gladness and joy shall they obtain, while sorrow and sighing shall have fled away.
12 “Ni kaɗai ne na ta’azantar da ku. Wane ne ku da kuke tsoron mutane masu mutuwa,’ya’yan mutane waɗanda suke ciyawa ne kawai,
I, I am he that comforteth you: who art thou, that thou shouldst be afraid of a mortal that must die, and of a son of man who will wither as the grass?
13 har da kuka manta da Ubangiji Mahaliccinku, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya, har kuna zama da tsoro kowace rana saboda fushin masu zalunci, waɗanda sun ƙudura sai sun hallaka? Gama ina fushin mai zalunci?
And thou forgettest the Lord, thy Maker, who hath spread out the heavens, and laid the foundations of the earth; and thou dreadest continually, all the day, because of the fury of the oppressor, whenever he aimeth to destroy: and where is [now] the fury of the oppressor?
14 Ba da daɗewa za a’yantar da’yan kurkuku; ba za su mutu a kurkuku ba, ba kuwa za su rasa abinci ba.
The exile will be speedily set free; and he shall not die in the dungeon, and his bread shall not fail.
15 Gama ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya dama teku domin raƙumansa su yi ruri, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
For I am the Lord thy God, who stirreth up the sea that its waves roar: the Lord of hosts is his name.
16 Na sa maganata a bakinka na kuma rufe ka da inuwar hannuna, Na shimfiɗa sammai, na kafa harsashen duniya, na kuma ce wa Sihiyona, ‘Ku mutanena ne.’”
And I have placed my words in thy mouth, and with the shadow of my hand have I covered thee: to plant the heavens, and to lay the foundations of the earth, and to say to Zion, Thou art my people.
17 Ki farka, ki farka! Ki tashi, ya Urushalima, ke da kika sha daga hannun Ubangiji kwaf na fushinsa, ke da kika shanye har ƙasar kwaf kwaf da ya sa mutane suna tangaɗi.
Rouse up, rouse up, arise, O Jerusalem, thou who hast drunk from the hand of the Lord the cup of his fury: the deep cup of confusion hast thou drunk, hast thou drained.
18 Cikin dukan’ya’yan da ta haifa; cikin dukan’ya’yan da ta yi reno babu wani da zai kama hannunta.
There is none to lead her, from all the children whom she hath born; and there is none that taketh her by the hand, from all the children whom she hath brought up.
19 Waɗannan masifu riɓi biyu sun auko miki, wa zai ta’azantar da ke? Lalaci da hallaka, yunwa da takobi, wa zai ƙarfafa ki?
Two things are these which have befallen thee: who will have compassion for thee? desolation and destruction, and famine and sword—with whom shall I comfort thee?
20 ’Ya’yanki sun sume; sun kwanta kusurwar kowane titi, kamar barewar da aka kama da tarko. Sun cika da fushin Ubangiji da kuma tsawatawar Allahnki.
Thy children have fainted, they lie at the entrance of all streets, as a wild bull caught in a net, [they are those] who are full of the fury of the Lord, the threatening of thy God.
21 Saboda haka ki ji wannan, ke mai wahala, wadda ta bugu, amma ba da ruwan inabi.
Therefore hear now this, O thou afflicted, and drunken, but not with wine.
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Allahnki, wanda ya kāre mutanensa, “Duba, na ƙwace daga hannunki kwaf da ya sa ki tangaɗi; daga wannan kwaf, kwaf na fushina, ba za ki ƙara sha ba.
Thus hath said thy Lord, the Eternal, and thy God, who will ever plead for his people, Behold, I have taken out of thy hand the cup of confusion, the deep cup of my fury: thou shalt never more drink it again.
23 Zan sa shi a hannuwan masu gwada miki azaba, waɗanda suke ce miki, ‘Fāɗi rubda ciki don mu iya taka a kanki.’ Kika kuma mai da bayanki kamar ƙasa, kamar titin da ake takawa a kai.”
And I will place it in the hand of those who have tortured thee, that have said to thy soul, Bend thee down, that we may pass over; and thou madest like the earth thy back, and like the street for those that passed over.