< Ishaya 50 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
Yahweh diz: “Onde está a conta do divórcio de sua mãe, com a qual eu a guardei? Ou a qual dos meus credores eu os vendi? Eis que você foi vendido por suas iniqüidades, e sua mãe foi presa por suas transgressões.
2 Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
Por que, quando eu cheguei, não havia ninguém? Quando eu liguei, por que não havia ninguém para responder? Minha mão está encurtada, que não pode redimir? Ou eu não tenho poder para entregar? Eis que, à minha repreensão, eu seco o mar. Eu faço dos rios uma região selvagem. Seus peixes fedem porque não há água, e morrem de sede.
3 Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
Eu visto os céus com negritude. Eu faço do pano de saco a sua cobertura”.
4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
O Senhor Yahweh me deu a língua daqueles que são ensinados, que eu possa saber sustentar com palavras aquele que está cansado. Ele desperta de manhã pela manhã, ele desperta meu ouvido para ouvir como aqueles que são ensinados.
5 Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
O Senhor Javé me abriu os ouvidos. Eu não era rebelde. Eu não voltei atrás.
6 Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
Eu dei minhas costas para aqueles que me venceram, e minhas bochechas para aqueles que arrancaram o cabelo. Eu não escondi meu rosto da vergonha e da cuspideira.
7 Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
Pois o Senhor Yahweh me ajudará. Portanto, não fiquei confundido. Por isso, coloquei meu rosto como uma pedra, e eu sei que não ficarei desapontado.
8 Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
He que me justifica está perto. Quem irá apresentar queixa contra mim? Vamos nos levantar juntos. Quem é meu adversário? Deixe-o chegar perto de mim.
9 Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
Eis que o Senhor Yahweh me ajudará! Quem será aquele que me condenará? Eis que todos eles envelhecerão como uma peça de vestuário. As traças as devorarão.
10 Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
Quem entre vocês teme Yahweh e obedece à voz de seu servo? Aquele que caminha na escuridão e não tem luz, deixá-lo confiar no nome de Yahweh, e confiar em seu Deus.
11 Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.
Eis, todos vocês que acendem uma fogueira, que se enfeitam com tochas ao redor de vocês mesmos, caminhar na chama de sua fogueira, e entre as tochas que você acendeu. Você terá isto da minha mão: você vai se deitar de tristeza.

< Ishaya 50 >