< Ishaya 50 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
Nanku okutshiwo nguThixo: “Ingaphi incwadi kanyoko yokuchitha umtshado engamxotsha ngayo na? Kumbe nguphi kwababelezikwelede zami engamthengisayo na? Lathengiswa ngenxa yezono zenu, lonyoko waliwa ngenxa yokona kwenu.
2 Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
Ekufikeni kwami, kungani kwakungelamuntu na? Ekubizeni kwami, kungani kungekho muntu owasabelayo na? Ingalo yami yayimfitshane kakhulu ukuba ilihlenge na? Angilamandla okulikhulula na? Ngokukhuza nje kuphela, ngiyalomisa ulwandle, ngiphendule imifula ibe yinkangala; inhlanzi zayo zibole ngenxa yokuswela amanzi, zife ngenxa yokoma.
3 Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
Ngembathisa umkhathi ngomnyama. Ngenze amasaka abe yisembeso sawo.”
4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
UThixo wobukhosi unginike ulimi olufundisiweyo ukuba ngazi ilizwi lokuqinisa abadiniweyo. Uyangivusa ekuseni kwansukuzonke, avuse indlebe yami ukuba ilalele njengofundiswayo.
5 Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
UThixo Wobukhosi uvule indlebe zami, njalo angizange ngibe ngohlamukayo; angibuyelanga emuva.
6 Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
Nganikela umhlana wami kulabo ababengitshaya, lezihlathi zami kulabo abacutha indevu zami; ubuso bami angibufihlanga ekugconweni lekukhafulelweni.
7 Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
Ngenxa yokuthi uThixo Wobukhosi uyangisiza angiyikuyangeka. Ngakho-ke sengiqinise ubuso bami babanjengelitshe lomlilo; njalo ngiyazi ukuthi angiyikuyangeka.
8 Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
Lowo ongimelayo useduzane. Ngubani-ke ongangethesa amacala? Kasiqondane. Ngubani ongimangalelayo na? Kangiqonde!
9 Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
NguThixo Wobukhosi ongisizayo. Ngubani lowo ongathi ngilecala na? Bonke bazaguga njengesigqoko, inondo izabadla.
10 Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
Ngubani phakathi kwenu omesabayo uThixo elalela ilizwi lenceku yakhe na? Lowo ohamba emnyameni, ongelakho ukukhanya, kathembe ebizweni likaThixo abambelele kuThixo wakhe.
11 Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.
Kodwa khathesi, lonke lina eliphemba imililo lizenzele amalangabi okukhanyisa, sukani, lihambe ekukhanyeni kwemililo yenu, lokwezibane elizikhanyisileyo. Elizakwamukela esandleni sami yilokhu: Lizalala phansi lisebuhlungwini.

< Ishaya 50 >