< Ishaya 50 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
Voici ce que dit le Seigneur: Quel est cet acte de répudiation donné à votre mère, par lequel je l’ai renvoyée? ou quel est mon créancier à qui je vous ai vendus? voilà que pour vos iniquités vous avez été vendus, et pour vos crimes, j’ai renvoyé votre mère.
2 Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
Parce que je suis venu, et il n’y avait pas un homme: j’ai appelé, et il n’y avait personne qui entendit; est-ce que ma main s’est raccourcie, et est devenue toute petite, en sorte que je ne puisse vous racheter? ou bien n’y a-t-il pas en moi de force pour délivrer? Voici qu’à ma réprimande je ferai un désert de la mer; je mettrai les fleuves à sec; les poissons pourriront faute d’eau, et périront de soif.
3 Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
J’envelopperai les cieux de ténèbres, et je leur mettrai un sac pour couverture.
4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
Le Seigneur m’a donné une langue savante, afin que je sache soutenir par la parole celui qui est abattu; il prépare dès le matin, dès le matin il prépare mon oreille, afin que je l’écoute comme un maître.
5 Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
Le Seigneur Dieu m’a ouvert l’oreille, et moi je ne le contredis pas; je ne me suis pas retiré en arrière.
6 Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
J’ai abandonné mon corps à ceux qui me frappaient, mes joues à ceux qui arrachaient ma barbe; je n’ai pas détourné ma face à ceux qui me réprimandaient et qui crachaient sur moi.
7 Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
Le Seigneur Dieu est mon aide; c’est pour cela que je n’ai pas été confondu; c’est pour cela que j’ai présenté ma face comme une pierre très dure, et je sais que je ne serai pas confondu.
8 Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
Près de moi est celui qui me justifie, qui me contredira? présentons-nous ensemble, qui est mon adversaire? qu’il s’approche de moi.
9 Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
Voici que le Seigneur Dieu est mon aide, qui est-ce qui me condamnera? voici que tous seront mis en pièces comme un vêtement, la teigne les rongera.
10 Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
Qui de vous craint le Seigneur, écoute la voix de son serviteur? que celui qui a marché dans les ténèbres et en qui n’est pas la lumière, espère au nom du Seigneur, et qu’il s’appuie sur son Dieu.
11 Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.
Voici que vous tous qui avez allumé un feu, qui êtes environnés de flammes, marchez à la lumière de votre feu. et dans les flammes que vous avez allumées; c’est par ma main que cela vous a été fait, vous dormirez au milieu des douleurs.

< Ishaya 50 >