< Ishaya 50 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
Thus saith Jehovah: Where is the bill of your mother's divorcement, By which I dismissed her? Or who is he among my creditors To whom I have sold you? Behold, for your iniquities are ye sold, And for your transgressions was your mother dismissed.
2 Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
Wherefore, when I came, was no man at hand? When I called, was there none to answer? Is my hand too short to redeem? Or have I no power to deliver? Behold, at my rebuke I dry up the sea, And make the rivers a desert. Their fish putrefy for want of water, And die with thirst.
3 Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
I clothe the heavens with blackness, And make sackcloth their covering.
4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
The Lord Jehovah hath given me the tongue of the learned, That I might know how to strengthen with my words them that are weary; He wakeneth me every morning, He wakeneth mine ear, That I may hear in the manner of the learned.
5 Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
The Lord Jehovah opened mine ear, And I was not disobedient, Neither did I withdraw myself backward.
6 Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
I gave my back to the smiters, And my cheeks to them that pluck the beard; I hid not my face from shame and spitting.
7 Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
But the Lord Jehovah is my helper, Therefore shall I not be confounded; Therefore have I made my face like a flint, For I know that I shall not be put to shame.
8 Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
He that defendeth my cause is near; Who will contend with me? Let us stand up together! Who is my adversary? Let him come near to me!
9 Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
Behold, the Lord Jehovah is my defender; Who is he that shall condemn me? Behold, they shall all waste away like a garment; The moth shall consume them.
10 Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
Who is there among you that feareth Jehovah, That hearkeneth to the voice of his servant, That walketh in darkness and hath no light? Let him trust in the name of Jehovah, And lean upon his God.
11 Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.
Behold, all ye who kindle a fire, Who gird yourselves with burning arrows! Walk ye in the light of your fire, And in the burning arrows which ye have kindled. This shall ye have from my hand; Ye shall lie down in sorrow.

< Ishaya 50 >