< Ishaya 50 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
Takto praví Hospodin: Kdež jest lístek zapuzení matky vaší, kterýmž jsem ji propustil? Aneb kdo jest z věřitelů mých, jemuž jsem vás prodal? Aj, nepravostmi svými prodali jste sebe, a pro převrácenosti vaše propuštěna jest matka vaše.
2 Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
Proč, když přicházím, není žádného, když volám, žádný se neozývá? Zdaliž jest naprosto ukrácena ruka má, aby nemohla vykoupiti? A žádné-liž není ve mně moci k vysvobození? Aj, žehráním svým vysušuji moře, obracím řeky v poušť, až se smrazují ryby jejich, proto že nebývá vody, a mrou žízní.
3 Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
Obláčím nebesa v smutek, a žíni dávám jim za oděv.
4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
Panovník Hospodin dal mi jazyk umělý, abych uměl příhodně ustalému mluviti slova. Probuzuje každého jitra, probuzuje mi uši, abych slyšel, tak jako pilně se učící.
5 Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
Panovník Hospodin otvírá mi uši, a já se nepostavuji zpurně, aniž se nazpět odvracím.
6 Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
Těla svého nastavuji bijícím, a líce svého rvoucím mne, tváři své neskrývám od pohanění a plvání.
7 Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
Nebo Panovník Hospodin spomáhá mi, pročež nebývám zahanben. Pro touž příčinu nastavuji tváři své jako škřemene; nebo vím, že nebudu zahanben.
8 Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
Blízkoť jest ten, kterýž mne ospravedlňuje. Kdož se nesnadniti bude se mnou? Postavme se spolu; kdo jest odpůrce můj, nechť přistoupí ke mně.
9 Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
Aj, Panovník Hospodin spomáhati mi bude. Kdož jest, ješto by mne potupil? Aj, všickni takoví jako roucho zvetšejí, mol sžíře je.
10 Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
Kdo jest mezi vámi, ješto se bojí Hospodina, poslouchej hlasu služebníka jeho. Kdo jest, ješto chodí v temnostech, a nemá žádného světla, doufej ve jméno Hospodinovo, a zpolehni na Boha svého.
11 Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.
Aj, vy všickni, kteříž zaněcujete oheň, a jiskrami se přepasujete, choďtež v blesku ohně svého, a v jiskrách, kteréž jste roznítili. Od ruky mé toto se vám stane, že v bolesti ležeti budete.

< Ishaya 50 >