< Ishaya 5 >

1 Zan rera waƙa wa ƙaunataccena waƙa game da gonar inabinsa. Ƙaunataccena yana da gonar inabi a gefen tudu mai dausayi.
اینک سرودی دربارهٔ محبوب خود و تاکستانش می‌سرایم: محبوب من تاکستانی بر تپه‌ای حاصلخیز داشت.
2 Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun ya shuka mata inabi mafi kyau. Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi. Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin, amma sai ga shi inabin ya ba da munanan’ya’ya.
او زمینش را کند و سنگهایش را دور ریخت، و بهترین درختان مو را در آن کاشت. درون آن برج دیدبانی ساخت، چرخشتی نیز در آن کند. چشم انتظار انگور نشست، اما تاکستانش انگور ترش آورد.
3 “Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda, ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
اکنون محبوب من می‌گوید: «ای اهالی اورشلیم و یهودا، شما در میان من و تاکستانم حکم کنید!
4 Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina fiye da abin da na yi mata? Da na nemi inabi masu kyau, me ya sa ta ba da munana’ya’ya?
دیگر چه می‌بایست برای تاکستان خود می‌کردم که نکردم؟ پس چرا وقتی منتظر انگور شیرین بودم، انگور ترش آورد؟
5 Yanzu zan faɗa muku abin da zan yi da gonar inabina. Zan cire katangar da ta kewaye ta, za tă kuwa lalace; zan rushe bangonta, za a kuwa tattake ta.
حال به شما می‌گویم با تاکستان خود چه خواهم کرد. من دیواری را که دورش کشیده‌ام، خراب خواهم کرد تا به چراگاه تبدیل شود و زیر پای حیوانات پایمال گردد.
6 Zan mai da ita kango, ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba, sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can Zan umarci gizagizai kada su yi ruwan sama a kanta.”
تاکستانم را دیگر هرس نخواهم کرد و زمینش را دیگر نخواهم کند. آن را وا می‌گذارم تا در آن خار و خس بروید و به ابرها دستور می‌دهم که دیگر بر آن نبارند.»
7 Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki ita ce gidan Isra’ila, mutanen Yahuda kuma su ne lambun farin cikinsa. Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini; yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
داستان تاکستان، داستان قوم خداوند لشکرهای آسمان است. بنی‌اسرائیل همان تاکستان هستند و مردم یهودا نهالهایی که خداوند با خشنودی در تاکستان خود نشاند. او از قوم خود انتظار انصاف داشت، ولی ایشان بر مردم ظلم و ستم روا داشتند. او انتظار عدالت داشت، اما فریاد مظلومان به گوشش می‌رسید.
8 Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje kuke kuma haɗa gonaki da gonaki har babu sauran filin da ya rage ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
وای بر شما که دائم خانه و مزرعه می‌خرید تا دیگر جایی برای دیگران نماند و خود به تنهایی در سرزمینتان ساکن شوید.
9 Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana, “Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango, za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
خداوند لشکرهای آسمان به من فرمود که این خانه‌های بزرگ و زیبا ویران و خالی از سکنه خواهند شد.
10 Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai, mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
از ده جریب تاکستان، یک بشکه شراب نیز به دست نخواهد آمد و ده من دانه، حتی یک من غله نیز نخواهد داد!
11 Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe don su nufi wurin shaye-shaye, waɗanda suke raba dare har sai sun bugu da ruwan inabi.
وای بر شما که صبح زود بلند می‌شوید و تا نیمه‌شب به عیش و نوش می‌پردازید.
12 Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu, ganguna da busa da ruwan inabi, amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba, ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
با بربط و چنگ، دف و نی و شراب محفل خود را گرم می‌کنید، اما به کارهای خداوند نمی‌اندیشید.
13 Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta domin rashin fahimi; manyan mutanensu za su mutu da yunwa talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
بنابراین، ای قوم من، به خاطر این نابخردی به سرزمینهای دور دست تبعید خواهید شد. رهبرانتان از گرسنگی و مردم عادی از تشنگی خواهند مرد.
14 Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol h7585)
دنیای مردگان با ولع زیاد دهان خود را باز کرده، تا آنها را به کام خود فرو برد. بزرگان و اشراف‌زادگان اورشلیم همراه مردم عادی که شادی می‌کنند، همگی طعمهٔ مرگ خواهند شد. (Sheol h7585)
15 Ta haka za a ƙasƙantar da mutum kuma za a ƙasƙantar da’yan adam, za a ƙasƙanta da masu girman kai.
در آن روز، متکبران پست خواهند شد و همه خوار و ذلیل خواهند گردید،
16 Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya, kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
اما خداوند لشکرهای آسمان برتر از همه خواهد بود، زیرا فقط او مقدّس، عادل و نیکوست.
17 Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu; raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
در آن روزها، حیوانات در میان ویرانه‌های دولتمندان اورشلیم خواهند چرید؛ آنجا چراگاه بره‌ها و گوساله‌ها و بزها خواهد شد.
18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
وای بر آنانی که مثل حیوانی که به گاری بسته شده باشد، گناهانشان را با طناب به دنبال خود می‌کشند،
19 waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta, bari yă hanzarta aikinsa don mu gani. Bari yă iso, bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo, don mu sani.”
و با تمسخر می‌گویند: «ای خدا، زود باش ما را تنبیه کن! می‌خواهیم ببینیم چه کاری از دستت برمی‌آید!»
20 Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta nagarta kuma mugunta, waɗanda suke mai da duhu haske haske kuma duhu, waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi zaƙi kuma ɗaci.
وای بر شما که خوب را بد و بد را خوب می‌دانید؛ تاریکی را به جای نور و نور را به جای تاریکی می‌گذارید، تلخی را شیرینی و شیرینی را تلخی می‌خوانید.
21 Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima da kuma wayo a idonsu.
وای بر شما که خود را دانا می‌پندارید و به نظر خود عاقل می‌نمایید؛
22 Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
وای بر شما که استادید اما نه در اجرای عدالت، بلکه در شرابخواری و میگساری!
23 waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci, amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
از بدکاران رشوه می‌گیرید و آنان را تبرئه می‌کنید و حق نیکوکاران را پایمال می‌نمایید.
24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta, haka saiwarsu za su ruɓa iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura; gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
بنابراین مانند کاه و علف خشک که در آتش می‌افتد و می‌سوزد، ریشه‌هایتان خواهد گندید و شکوفه‌هایتان خشک خواهد شد، زیرا قوانین خداوند لشکرهای آسمان را دور انداخته، کلام خدای مقدّس اسرائیل را خوار شمرده‌اید.
25 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
خداوند بر قوم خود خشمناک است و دست خود را دراز کرده تا ایشان را مجازات کند. تپه‌ها به لرزه در می‌آیند، و لاشه‌های مردم مثل زباله در خیابانها انداخته می‌شوند. با وجود این، خشم و غضب او پایان نمی‌یابد و او دست از مجازات ایشان برنمی‌دارد.
26 Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa, ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya. Ga shi sun iso, da sauri da kuma gaggawa!
خداوند قومهایی را از دور دست فرا خواهد خواند تا به اورشلیم بیایند. آنها به سرعت خواهند آمد
27 Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe, babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci; babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi, ba igiyar takalmin da ta tsinke.
و در راه خسته نخواهند شد و پایشان نخواهد لغزید و توقف نخواهند کرد. کمربندها و بند کفشهایشان باز نخواهند شد. خواهند دوید بدون آنکه استراحت کنند یا بخوابند.
28 Kibiyoyinsu masu tsini ne, an ɗaura dukan bakkunansu; kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
تیرهایشان تیز و کمانهایشان خمیده است. سم اسبهای ایشان مانند سنگ خارا محکم است و چرخهای ارابه‌هایشان مثل گردباد می‌چرخند.
29 Rurinsu ya yi kamar na zaki, suna ruri kamar’yan zakoki; suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
ایشان چون شیر می‌غرند و بر سر شکار فرود می‌آیند و آن را با خود به جایی می‌برند که کسی نتواند از چنگشان نجات دهد.
30 A wannan rana za su yi ta ruri a kansa kamar rurin teku. Kuma in wani ya dubi ƙasar, zai ga duhu da damuwa; haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.
در آن روز، آنها مانند دریای خروشان بر سر قوم من خواهند غرید و تاریکی و اندوه سراسر اسرائیل را فرا خواهد گرفت و آسمان آن تیره خواهد شد.

< Ishaya 5 >