< Ishaya 5 >

1 Zan rera waƙa wa ƙaunataccena waƙa game da gonar inabinsa. Ƙaunataccena yana da gonar inabi a gefen tudu mai dausayi.
Jeg vil synge om min elskede, synge min venns sang om hans vingård. Min venn hadde en vingård på en fruktbar haug.
2 Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun ya shuka mata inabi mafi kyau. Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi. Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin, amma sai ga shi inabin ya ba da munanan’ya’ya.
Og han gravde den om og renset den for sten og plantet edle vintrær i den og bygget et tårn i dens midte og hugg også ut en perse i den; og han ventet at den skulde bære gode druer, men den bar ville.
3 “Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda, ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
Og nu, I Jerusalems innbyggere og Judas menn, døm mellem mig og min vingård!
4 Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina fiye da abin da na yi mata? Da na nemi inabi masu kyau, me ya sa ta ba da munana’ya’ya?
Hvad var det mere å gjøre med min vingård, som jeg ikke har gjort med den? Hvorfor bar den ville druer når jeg ventet at den skulde bære gode?
5 Yanzu zan faɗa muku abin da zan yi da gonar inabina. Zan cire katangar da ta kewaye ta, za tă kuwa lalace; zan rushe bangonta, za a kuwa tattake ta.
Så vil jeg nu la eder vite hvad jeg vil gjøre med min vingård: Jeg vil ta bort dens gjerde, så den blir avgnaget; jeg vil rive ned dens mur, så den blir nedtrådt.
6 Zan mai da ita kango, ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba, sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can Zan umarci gizagizai kada su yi ruwan sama a kanta.”
Og jeg vil la den ligge øde; den skal ikke skjæres og ikke hakkes, så den skyter op i torn og tistel, og skyene vil jeg byde at de ikke skal la regn falle på den.
7 Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki ita ce gidan Isra’ila, mutanen Yahuda kuma su ne lambun farin cikinsa. Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini; yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
For Herrens, hærskarenes Guds vingård er Israels hus, og Judas menn hans kjæreste plantning; og han ventet rett, men se, der er blodsutgydelse; han ventet rettferdighet, men se, der er skrik.
8 Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje kuke kuma haɗa gonaki da gonaki har babu sauran filin da ya rage ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
Ve eder som legger hus til hus og mark til mark, inntil det ikke er mere rum tilbake, så I blir boende alene i landet.
9 Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana, “Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango, za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
I mine ører lyder det fra Herren, hærskarenes Gud: Sannelig, mange hus skal bli øde, store og gode hus skal stå tomme;
10 Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai, mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
for en vingård på ti dagers plogland skal gi en bat, og en homers utsæd skal gi en efa.
11 Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe don su nufi wurin shaye-shaye, waɗanda suke raba dare har sai sun bugu da ruwan inabi.
Ve dem som står tidlig op om morgenen og jager efter sterk drikk, som sitter langt utover aftenen, glødende av vin!
12 Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu, ganguna da busa da ruwan inabi, amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba, ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
Citar og harpe, pauke og fløite og vin har de i sine drikkelag; men Herrens verk ser de ikke, og hans henders gjerning har de ikke øie for.
13 Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta domin rashin fahimi; manyan mutanensu za su mutu da yunwa talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
Derfor blir mitt folk bortført uforvarende, dets stormenn lider hunger, og dets larmende hop vansmekter av tørst.
14 Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol h7585)
Derfor blir dødsriket ennu grådigere og spiler op sin munn umåtelig, og ned farer byens fornemme og dens larmende hop og dens buldrende sverm og alle som jubler i den. (Sheol h7585)
15 Ta haka za a ƙasƙantar da mutum kuma za a ƙasƙantar da’yan adam, za a ƙasƙanta da masu girman kai.
Og mennesket blir bøiet, og mannen ydmyket, og de overmodiges øine blir ydmyket.
16 Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya, kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
Og høi blir Herren, hærskarenes Gud, ved dommen, og den hellige Gud viser sig hellig ved rettferdighet.
17 Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu; raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
Og lam skal beite der som på sin egen mark, og de rikes jord legges øde og fortæres av fremmede.
18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
Ve dem som drar på misgjerningen med løgnens tauger og på synden som med vognrep,
19 waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta, bari yă hanzarta aikinsa don mu gani. Bari yă iso, bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo, don mu sani.”
de som sier: La ham skynde sig, la ham haste med sin gjerning, så vi kan få se den! La det råd som Israels Hellige har tatt, nærme sig, la det komme, så vi kan lære det å kjenne!
20 Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta nagarta kuma mugunta, waɗanda suke mai da duhu haske haske kuma duhu, waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi zaƙi kuma ɗaci.
Ve dem som kaller det onde godt og det gode ondt, som gjør mørke til lys og lys til mørke, som gjør bittert til søtt og søtt til bittert!
21 Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima da kuma wayo a idonsu.
Ve dem som er vise i egne øine og forstandige i egne tanker!
22 Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
Ve dem som er helter til å drikke vin og dyktige til å blande sterk drikk,
23 waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci, amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
de som for gave gir rett til den som har urett, og tar retten fra de rettferdige!
24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta, haka saiwarsu za su ruɓa iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura; gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Derfor, som ilden fortærer halm, og høi synker sammen i luen, så skal deres rot råtne, og deres blomst fare op som støv; for de har forkastet Herrens, hærskarenes Guds lov og foraktet Israels Helliges ord.
25 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
Derfor optendes Herrens vrede over hans folk, og han rekker ut sin hånd mot det og slår det, så fjellene bever, og likene ligger som skarnet midt på gatene. Men med alt dette vender hans vrede ikke tilbake, og ennu er hans hånd rakt ut.
26 Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa, ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya. Ga shi sun iso, da sauri da kuma gaggawa!
Og han løfter et banner for hedningefolkene langt borte og piper fienden hit fra jordens ende; og se, hastig og lett kommer han.
27 Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe, babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci; babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi, ba igiyar takalmin da ta tsinke.
Der er ingen trett og ingen som snubler blandt dem, ingen som blunder eller sover; beltet om lendene går ikke op, og ingen skorem sønderrives.
28 Kibiyoyinsu masu tsini ne, an ɗaura dukan bakkunansu; kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
Fiendens piler er hvesset, og alle hans buer spent; hans hesters hover kan lignes med flintesten, og hans vognhjul er som stormvinden.
29 Rurinsu ya yi kamar na zaki, suna ruri kamar’yan zakoki; suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
Hans brøl er som løvinnens, han brøler som de unge løver og brummer og griper sitt rov og bærer det bort, og der er ingen som redder.
30 A wannan rana za su yi ta ruri a kansa kamar rurin teku. Kuma in wani ya dubi ƙasar, zai ga duhu da damuwa; haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.
Og det bruser over det på den dag, likesom havet bruser; og skuer en til jorden, se, da er det mørke! Trengsel og lys! Det blir mørkt på dets skydekte himmel.

< Ishaya 5 >