< Ishaya 5 >

1 Zan rera waƙa wa ƙaunataccena waƙa game da gonar inabinsa. Ƙaunataccena yana da gonar inabi a gefen tudu mai dausayi.
Let me sing, I pray you, for a well-beloved of mine, The song of my beloved concerning his vineyard: —A vineyard, had my well-beloved on a very fruitful hill;
2 Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun ya shuka mata inabi mafi kyau. Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi. Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin, amma sai ga shi inabin ya ba da munanan’ya’ya.
And he thoroughly digged it, And gathered out the stones thereof, And planted it with a precious vine, And built a tower in the midst thereof, Moreover also a wine-press, hewed he therein, —Then waited he that it should bring forth grapes. And it brought forth wild grapes:
3 “Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda, ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
Now, therefore, O inhabitant of Jerusalem, And men of Judah, —Judge, I pray you, betwixt me, and my vineyard: —
4 Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina fiye da abin da na yi mata? Da na nemi inabi masu kyau, me ya sa ta ba da munana’ya’ya?
What could have been done further to my vineyard, That I had not done in it? Why then—When I had waited that it should bring forth grapes, Brought it forth, wild grapes?
5 Yanzu zan faɗa muku abin da zan yi da gonar inabina. Zan cire katangar da ta kewaye ta, za tă kuwa lalace; zan rushe bangonta, za a kuwa tattake ta.
Now, therefore, I pray you, let me tell, you, what I am about to do to my vineyard, —To take away the fence thereof And it shall be eaten up, To destroy the wall thereof And it shall be trodden down;
6 Zan mai da ita kango, ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba, sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can Zan umarci gizagizai kada su yi ruwan sama a kanta.”
And I will make it a waste; —It shall be neither pruned nor hoed, But there shall come up briars and thorns, —And upon the clouds, will I lay a charge, That they rain thereon no rain.
7 Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki ita ce gidan Isra’ila, mutanen Yahuda kuma su ne lambun farin cikinsa. Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini; yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
Surely the vineyard of Yahweh of hosts, is the house of Israel, And, the men of Judah, are the plantation in which he dearly delighted, —And he waited, For equity but lo! murderous iniquity, For the rule of right but lo the cry of the wronged.
8 Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje kuke kuma haɗa gonaki da gonaki har babu sauran filin da ya rage ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
Alas for them who join house to house, Field to field, bring they near, —Until there is no room, But ye are left to dwell alone in the midst of the land.
9 Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana, “Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango, za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
In mine ears, [said] Yahweh of hosts, —Verily, houses in abundance, shall become, a desolation, Large and fair, without inhabitant;
10 Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai, mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
For, ten yokes of vineyard, shall yield one bath, —And the seed of a homer, shall yield an ephah,
11 Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe don su nufi wurin shaye-shaye, waɗanda suke raba dare har sai sun bugu da ruwan inabi.
Alas, for them who rise early in the morning that strong drink, they may pursue, —Who follow on in the evening cool [until] with wine, they are heated;
12 Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu, ganguna da busa da ruwan inabi, amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba, ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
And it cometh to pass—that lyre and harp, timbrel and flute and wine are in their banquets, —But, the doing of Yahweh, they do not discern, And the work of his hands, have they not seen.
13 Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta domin rashin fahimi; manyan mutanensu za su mutu da yunwa talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
Therefore, are my people taken away captive before they know it, —And their honourable men are famished with hunger, And, their multitude, do gape for thirst.
14 Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol h7585)
Therefore, hath hades enlarged her desire, And opened her mouth to its widest, —And their glory, and their multitude and their pomp. and he that is uproarious shall descend thereinto. (Sheol h7585)
15 Ta haka za a ƙasƙantar da mutum kuma za a ƙasƙantar da’yan adam, za a ƙasƙanta da masu girman kai.
And the mean man hath been bowed down And the mighty man hath been humbled, —Yea the looks of the haughty shall be humbled.
16 Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya, kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
But Yahweh of hosts, hath been exalted, in justice, —And the GOD that is holy hath been hallowed in righteousness;
17 Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu; raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
Then shall the young rams feed where they please, —And, the wastes of the wealthy, shall strangers consume.
18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
Alas! for them Who draw on themselves punishment with cords of falsehood, —And as with waggon-bands, penalty:
19 waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta, bari yă hanzarta aikinsa don mu gani. Bari yă iso, bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo, don mu sani.”
Who say—Let his work quicken—let it hasten, That we may see, —And let the purpose of Israel’s Holy One, draw near and come. That we may know!
20 Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta nagarta kuma mugunta, waɗanda suke mai da duhu haske haske kuma duhu, waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi zaƙi kuma ɗaci.
Alas! for them Who call evil good and good evil, —Who put darkness for light and light for darkness, Who put bitter for sweet and sweet for bitter.
21 Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima da kuma wayo a idonsu.
Alas for them Who are wise in their own eyes, —And in their own sight, are prudent.
22 Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
Alas for them Who are heroes to drink wine, —And men of valour to mingle strong drink,
23 waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci, amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
Who justify the lawless, for a bribe, —Whereas the righteousness of the righteous, they take from him.
24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta, haka saiwarsu za su ruɓa iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura; gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Therefore, As a tongue of fire, eateth up straw, And a flame reduceth, dry grass, to powder, Their root, like rottenness, shall become, And their blossom, like dust shall ascend, —Because they refused the law of Yahweh of hosts, And the utterance of the Holy One of Israel, they despised.
25 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
For this cause, did the anger of Yahweh kindle upon his own people, And he stretched out his hand against them and smote them—So that the mountains, trembled, And, their dead bodies, served, for fuel in the midst of the streets. For all this, hath his anger, not turned back, But still, is his hand outstretched,
26 Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa, ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya. Ga shi sun iso, da sauri da kuma gaggawa!
Therefore will he lift up an ensign to the nations afar off, And signal for him from the end of the earth, —And lo! with hot haste, will he come:
27 Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe, babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci; babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi, ba igiyar takalmin da ta tsinke.
None shall be weary, and none shall stumble in his midst, He shall neither slumber nor sleep, —Nor shall be loosened, the girdle of his loins, Nor snapped, the thong of his sandals:
28 Kibiyoyinsu masu tsini ne, an ɗaura dukan bakkunansu; kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
Whose arrows, are sharpened, and all his bows, bent, —The hoofs of his horses, like flint, are accounted, And, his wheels, [are] like a storm-wind:
29 Rurinsu ya yi kamar na zaki, suna ruri kamar’yan zakoki; suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
A roar, hath he, like a lioness, —He will roar like wild lions—And will growl, and lay hold on prey, and carry into safety, and there be none to deliver.
30 A wannan rana za su yi ta ruri a kansa kamar rurin teku. Kuma in wani ya dubi ƙasar, zai ga duhu da damuwa; haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.
Yea he will growl at him in that day, like the growling of the sea, —Though he look hard for the land, lo! the darkness of distress, Yea the light, hath grown dark in its clouds!

< Ishaya 5 >