< Ishaya 5 >

1 Zan rera waƙa wa ƙaunataccena waƙa game da gonar inabinsa. Ƙaunataccena yana da gonar inabi a gefen tudu mai dausayi.
Let me sing for my well-beloved a song of my beloved concerning his vineyard. My well-beloved had a vineyard in a very fruitful hill.
2 Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun ya shuka mata inabi mafi kyau. Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi. Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin, amma sai ga shi inabin ya ba da munanan’ya’ya.
And he dug it, and gathered out the stones of it, and planted it with the choicest vine, and built a tower in the midst of it, and also hewed out a winepress in it. And he looked that it should bring forth grapes, and it brought forth wild grapes.
3 “Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda, ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
And now, O inhabitants of Jerusalem and men of Judah, judge, I pray you, between me and my vineyard.
4 Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina fiye da abin da na yi mata? Da na nemi inabi masu kyau, me ya sa ta ba da munana’ya’ya?
What could have been done more to my vineyard that I have not done in it? Why, when I looked that it should bring forth grapes, it brought forth wild grapes?
5 Yanzu zan faɗa muku abin da zan yi da gonar inabina. Zan cire katangar da ta kewaye ta, za tă kuwa lalace; zan rushe bangonta, za a kuwa tattake ta.
And now I will tell you what I will do to my vineyard. I will take away the hedge of it, and it shall be eaten up. I will break down the wall of it, and it shall be trodden down.
6 Zan mai da ita kango, ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba, sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can Zan umarci gizagizai kada su yi ruwan sama a kanta.”
And I will lay it waste. It shall not be pruned nor hoed, but there shall come up briers and thorns. I will also command the clouds that they rain no rain upon it.
7 Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki ita ce gidan Isra’ila, mutanen Yahuda kuma su ne lambun farin cikinsa. Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini; yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
For the vineyard of Jehovah of hosts is the house of Israel, and the men of Judah his pleasant plant. And he looked for justice, but behold, oppression, for righteousness, but behold, a cry.
8 Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje kuke kuma haɗa gonaki da gonaki har babu sauran filin da ya rage ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
Woe to those who join house to house, who lay field to field, till there is no room, and ye be made to dwell alone in the midst of the land!
9 Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana, “Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango, za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
In my ears says Jehovah of hosts, of a truth many houses shall be desolate, even great and fair, without inhabitant.
10 Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai, mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
For ten acres of vineyard shall yield one bath, and a homer of seed shall yield but an ephah.
11 Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe don su nufi wurin shaye-shaye, waɗanda suke raba dare har sai sun bugu da ruwan inabi.
Woe to those who rise up early in the morning, that they may follow strong drink, who tarry late into the night, till wine inflame them!
12 Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu, ganguna da busa da ruwan inabi, amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba, ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
And the harp and the lute, the tambourine and the pipe, and wine, are in their feasts, but they do not regard the work of Jehovah, nor have they considered the operation of his hands.
13 Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta domin rashin fahimi; manyan mutanensu za su mutu da yunwa talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
Therefore my people have gone into captivity for lack of knowledge, and their honorable men are famished, and their multitude are parched with thirst.
14 Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol h7585)
Therefore Sheol has enlarged its desire, and opened its mouth without measure. And their glory, and their multitude, and their pomp, and he who rejoices among them, descend into it. (Sheol h7585)
15 Ta haka za a ƙasƙantar da mutum kuma za a ƙasƙantar da’yan adam, za a ƙasƙanta da masu girman kai.
And the common man is bowed down, and the great man is debased, and the eyes of the lofty are humbled,
16 Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya, kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
but Jehovah of hosts is exalted in justice, and God the Holy One is sanctified in righteousness.
17 Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu; raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
Then the lambs shall feed as in their pasture, and wanderers shall eat the waste places of the fat ones.
18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
Woe to those who draw iniquity with cords of falsehood, and sin as it were with a cart rope,
19 waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta, bari yă hanzarta aikinsa don mu gani. Bari yă iso, bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo, don mu sani.”
who say, Let him make speed, let him hasten his work, that we may see it. And let the counsel of the Holy One of Israel draw near and come, that we may know it!
20 Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta nagarta kuma mugunta, waɗanda suke mai da duhu haske haske kuma duhu, waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi zaƙi kuma ɗaci.
Woe to those who call evil good, and good evil, who put darkness for light, and light for darkness, who put bitter for sweet, and sweet for bitter!
21 Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima da kuma wayo a idonsu.
Woe to those who are wise in their own eyes, and prudent in their own sight!
22 Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
Woe to those who are mighty to drink wine, and men of strength to mingle strong drink,
23 waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci, amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
who justify the wicked for rewards, and take away the justice of the righteous man from him!
24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta, haka saiwarsu za su ruɓa iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura; gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Therefore as the tongue of fire devours the stubble, and as the dry grass sinks down in the flame, so their root shall be as rottenness, and their blossom shall go up as dust, because they have rejected the law of Jehovah of hosts, and despised the word of the Holy One of Israel.
25 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
Therefore the anger of Jehovah is kindled against his people, and he has stretched forth his hand against them, and has smitten them. And the mountains tremble, and their dead bodies are as refuse in the midst of the streets. For all this his anger is not turned away, but his hand is stretched out still.
26 Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa, ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya. Ga shi sun iso, da sauri da kuma gaggawa!
And he will lift up an ensign to the nations from far, and will whistle for them from the end of the earth, and, behold, they shall come with speed swiftly.
27 Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe, babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci; babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi, ba igiyar takalmin da ta tsinke.
None shall be weary nor stumble among them. None shall slumber nor sleep, nor shall the belt of their loins be loosed, nor the latchet of their shoes be broken,
28 Kibiyoyinsu masu tsini ne, an ɗaura dukan bakkunansu; kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
whose arrows are sharp, and all their bows bent. Their horses' hoofs shall be accounted as flint, and their wheels as a whirlwind.
29 Rurinsu ya yi kamar na zaki, suna ruri kamar’yan zakoki; suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
Their roaring shall be like a lioness. They shall roar like young lions. Yea, they shall roar, and lay hold of the prey, and carry it away safe, and there shall be none to deliver.
30 A wannan rana za su yi ta ruri a kansa kamar rurin teku. Kuma in wani ya dubi ƙasar, zai ga duhu da damuwa; haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.
And they shall roar against them in that day like the roaring of the sea. And if a man looks to the land, behold, darkness and distress, and the light is darkened in the clouds of it.

< Ishaya 5 >