< Ishaya 49 >
1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Ouça, ilhas, para mim. Ouçam, povos, de longe: Yahweh me chamou do ventre; de dentro de minha mãe, ele mencionou meu nome.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
Ele fez minha boca como uma espada afiada. Ele me escondeu na sombra de sua mão. Ele me fez um eixo polido. Ele me manteve por perto em sua aljava.
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
Ele me disse: “Você é meu servo”, Israel, em quem eu serei glorificado”.
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
Mas eu disse: “Eu trabalhei em vão. Eu gastei minhas forças em vão para nada; mas certamente a justiça que me é devida está com Yahweh, e minha recompensa com meu Deus”.
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
Agora Yahweh, aquele que me formou desde o ventre para ser seu servo, diz para trazer Jacob de novo até ele, e para reunir Israel a ele, pois sou honrado aos olhos de Yahweh, e meu Deus se tornou minha força.
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
De fato, ele diz: “É muito leve uma coisa que você deveria ser meu servo para criar as tribos de Jacob”, e para restaurar os preservados de Israel. Eu também lhes darei luz para as nações, que você possa ser minha salvação até o fim da terra”.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Yahweh, o Redentor de Israel, e seu Santo, diz a quem o homem despreza, a quem a nação abomina, a um servo dos governantes: “Os reis devem ver e se erguer, príncipes, e eles devem adorar, por causa de Yahweh que é fiel, mesmo o Santo de Israel, que o escolheu”.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Yahweh diz: “Respondi-lhe em um tempo aceitável”. Eu o ajudei em um dia de salvação. Eu o preservarei e lhe darei por um pacto do povo, para erguer a terra, para fazê-los herdar a herança desolada,
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
dizendo para aqueles que estão vinculados, “Saiam! para aqueles que estão na escuridão, “Mostrem-se! “Eles devem se alimentar ao longo dos caminhos, e suas pastagens devem estar em todas as alturas sem árvores.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
Eles não terão fome nem sede; nem o calor nem o sol os atingirão, pois quem tem piedade deles, os conduzirá. Ele os guiará por nascentes de água.
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
Eu farei de todas as minhas montanhas uma estrada, e minhas estradas devem ser exaltadas.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Eis que estas devem vir de longe, e eis que estes vêm do norte e do oeste, e estes da terra de Sinim”.
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
Cantem, céus, e alegres, terra! Cantem, montanhas! Pois Yahweh tem confortado seu povo, e terá compaixão de sua aflição.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Mas Zion disse: “Yahweh me abandonou”, e o Senhor se esqueceu de mim”.
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
“Uma mulher pode esquecer seu filho lactante, que ela não deveria ter compaixão pelo filho de seu ventre? Sim, estes podem esquecer, no entanto, não me esquecerei de você!
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Eis que eu o gravei nas palmas das minhas mãos. Suas paredes estão continuamente diante de mim.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Seus filhos se apressam. Seus destruidores e aqueles que o devastaram o deixarão.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Levante os olhos para todos os lados e veja: todos eles se reúnem, e vêm até você. Como eu vivo”, diz Yahweh, “você certamente se vestirá com todos eles como com um ornamento, e se veste com eles, como uma noiva.
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
“Pois, quanto aos seus resíduos e seus lugares desolados, e sua terra que foi destruída, certamente agora essa terra será pequena demais para os habitantes, e aqueles que o engoliram estarão longe.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
As crianças de seu luto dirão em seus ouvidos, “Este lugar é muito pequeno para mim. Dê-me um lugar para morar”.
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
Então você dirá em seu coração: 'Quem concebeu isto para mim, desde que fui enlutado de meus filhos e estou sozinho, um exilado e vagando para frente e para trás? Quem os criou? Eis que eu fiquei sozinho. Onde estavam estes?”
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
O Senhor Javé diz: “Eis que levantarei minha mão para as nações”, e levanto minha bandeira para os povos. Eles trarão seus filhos em seu seio, e suas filhas devem ser carregadas nos ombros.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
Os reis devem ser seus pais adotivos, e suas rainhas suas mães lactantes. Eles se curvarão diante de você com o rosto voltado para a terra, e lamber a poeira de seus pés. Então você saberá que eu sou Yahweh; e aqueles que esperam por mim não ficarão desapontados”.
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Será retirado o saque dos poderosos, ou os prisioneiros legítimos serão entregues?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
Mas Yahweh diz: “Até os cativos dos poderosos serão levados”, e o saque recuperado dos ferozes, pois eu lutarei com aquele que lutar com você e eu salvarei seus filhos.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Alimentarei com sua própria carne aqueles que o oprimem; e serão embriagados com seu próprio sangue, como no vinho doce. Então toda a carne saberá que eu, Yahweh, sou seu Salvador e seu Redentor, o Poderoso de Jacob”.