< Ishaya 49 >

1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Hør på mig, I øer, og gi akt, I folk fra det fjerne! Herren har kalt mig fra mors liv av, han har nevnt mitt navn fra min mors skjød.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
Han har gjort min munn til et skarpt sverd og skjult mig i sin hånds skygge; han har gjort mig til en blank pil og gjemt mig i sitt kogger.
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
Og han sa til mig: Du er min tjener, du er Israel, på hvem jeg vil åpenbare min herlighet.
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
Men jeg sa: Forgjeves har jeg arbeidet mig trett, og til ingen nytte har jeg fortært min kraft; men min rett er allikevel hos Herren, og min lønn hos min Gud.
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
Og nu sier Herren, som fra mors liv har dannet mig til sin tjener, for å føre Jakob tilbake til ham og samle Israel for ham, og jeg er æret i Herrens øine, og min Gud er blitt min styrke -
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
han sier: Det er for lite at du er min tjener til å gjenreise Jakobs stammer og føre den frelste rest av Israel tilbake; så vil jeg da gjøre dig til hedningenes lys, forat min frelse må nå til jordens ende.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Så sier Herren, Israels gjenløser, Israels Hellige, til ham som er foraktet av hver sjel, til ham som vekker folks avsky, til ham som er herskeres tjener: Konger skal se det og reise sig, fyrster skal se det og kaste sig ned, for Herrens skyld, som er trofast, for Israels Helliges skyld, som utvalgte dig.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Så sier Herren: På den tid som behager mig, bønnhører jeg dig, og på frelsens dag hjelper jeg dig, og jeg vil bevare dig og gjøre dig til en pakt for folket, forat du skal gjenreise landet og utskifte de øde arvelodder
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
og si til de fangne: Gå ut! - til dem som er i mørket: Kom frem! På veiene skal de beite, og på alle de bare hauger skal det være beitemark for dem.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
De skal ikke sulte og ikke tørste, og hverken det glødende sandhav eller solen skal skade dem; for han som forbarmer sig over dem, skal føre dem og lede dem til kildevell,
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
og jeg vil gjøre alle mine fjell til veier, og mine ryddede veier skal bygges høiere.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Se, de kommer langt borte fra, nogen fra nord og nogen fra vest og nogen fra Sinims land.
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
Juble, I himler, og fryd dig, du jord! I fjell, bryt ut i frydesang! For Herren trøster sitt folk, og over sine elendige forbarmer han sig.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Sion sa: Herren har forlatt mig, Herren har glemt mig.
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
Glemmer vel en kvinne sitt diende barn, så hun ikke forbarmer sig over sitt livs sønn? Om også de glemmer, så glemmer ikke jeg dig.
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Se, I begge mine hender har jeg tegnet dig, dine murer står alltid for mig.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Dine barn kommer i hast; de som brøt dig ned og ødela dig, de skal dra bort fra dig.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Løft dine øine og se dig omkring! De samler sig alle sammen, de kommer til dig. Så sant jeg lever, sier Herren, du skal iføre dig dem alle sammen som en prydelse og binde dem om dig lik bruden;
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
for dine ruiner og dine øde steder og ditt herjede land - sannelig, nu skal du være for trang for innbyggerne, og dine ødeleggere skal være langt borte.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
Ennu skal du få høre barna fra din barnløshets dager si: Plassen er for trang for mig; flytt dig, så jeg kan få bo her!
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
Og du skal si i ditt hjerte: Hvem har født mig disse barn? Jeg var jo barnløs og ufruktbar, landflyktig og jaget bort. Og hvem har fostret disse? Jeg var jo enslig tilbake. Hvor var da disse?
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg vil løfte min hånd til hedningene og reise mitt banner for folkene, og de skal komme med dine sønner ved barmen, og dine døtre skal de bære på skulderen.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
Og konger skal være dine fosterfedre, og deres dronninger dine ammer; de skal kaste sig på sitt ansikt til jorden for dig, og dine føtters støv skal de slikke, og du skal kjenne at jeg er Herren, og at de som bier efter mig, ikke skal bli til skamme.
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Kan vel nogen ta hærfanget fra en kjempe, eller kan fangene slippe fra den som de med rette tilhører?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
Ja! For så sier Herren: Både skal fangene tas fra kjempen, og voldsmannens hærfang slippe unda, og med din motpart vil jeg gå i rette, og dine barn vil jeg frelse.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Og jeg vil la dine undertrykkere ete sitt eget kjøtt, og av sitt eget blod skal de bli drukne som av druesaft; og alt kjød skal kjenne at jeg, Herren, er din frelser, Jakobs Veldige din gjenløser.

< Ishaya 49 >