< Ishaya 49 >

1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Ecoutez, îles, et soyez attentifs, peuples éloignés: le Seigneur dès le sein m’a appelé, dès les entrailles de ma mère il s’est souvenu de mon nom.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
Il a disposé ma bouche comme un glaive aigu; à l’ombre de sa main il m’a protégé, et il m’a disposé comme une flèche choisie; il m’a caché dans son carquois.
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
Et il m’a dit: Mon serviteur, c’est toi, Israël, parce qu’en toi je me glorifierai.
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
Et moi j’ai dit: C’est dans le vide que j’ai travaillé, c’est sans motif et vainement que j’ai consumé ma force; ainsi mon jugement est au pouvoir du Seigneur, et mon travail au pouvoir de Dieu.
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
Et maintenant, dit le Seigneur, qui m’a formé dès le sein de ma mère pour le servir, afin que je ramène Jacob à lui, et Israël ne sera pas rassemblé, et j’ai été glorifié aux yeux du Seigneur, et mon Dieu est devenu ma force.
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
Il a donc dit: C’est peu que tu me serves à relever les tribus de Jacob, et à convertir les restes d’Israël. Voici que je t’ai posé en lumière des nations, afin que tu sois mon salut jusqu’à l’extrémité de la terre.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Voici ce que dit le Seigneur, le rédempteur d’Israël, son saint, à une âme méprisable, à une nation détestée, à l’esclave de ceux qui le dominent: Les rois te verront, et les princes se lèveront, et ils l’adoreront à cause du Seigneur, parce qu’il est fidèle, et à cause du saint d’Israël qui t’a choisi.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Voici ce que dit le Seigneur: En un temps favorable je t’ai exaucé, et en un jour de salut je t’ai secouru, je t’ai conservé, et je t’ai établi pour faire alliance avec un peuple, afin que tu rétablisses une terre, et que tu possèdes des héritages dissipés;
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
Afin que tu dises à ceux qui étaient dans les fers: Sortez; et à ceux qui étaient dans les ténèbres: Venez à la lumière. Sur les chemins, ils trouveront à paître, et dans toutes les plaines seront leurs pâturages.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
Ils n’auront pas faim, ni soif; la chaleur ne les atteindra pas, ni le soleil; parce que celui qui a pitié d’eux les conduira, et à des sources d’eaux il les fera boire.
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
Et je disposerai toutes mes montagnes en une voie, et mes sentiers seront élevés.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Voici que ceux-ci viendront de loin, et voici que ceux-là viendront de l’aquilon et de la mer, et ceux-ci de la terre du midi.
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
Louez, cieux; exulte, terre; montagnes, faites retentir la louange, parce que le Seigneur a consolé son peuple, et qu’il aura pitié de ses pauvres.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Et Sion a dit: Le Seigneur m’a abandonnée, et le Seigneur m’a oubliée.
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
Est-ce qu’une mère peut oublier son enfant, de sorte qu’elle n’ait pas pitié du fils de son sein? mais quand même elle l’oublierait, pour moi, je ne l’oublierai point.
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Voici que je t’ai gravée dans mes mains; tes murs sont devant mes yeux sans cesse.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Ils sont venus, tes constructeurs; ceux qui te détruisaient et te dissipaient, sortiront de ton enceinte.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Lève tes yeux tout autour et vois; tous ceux-ci se sont rassemblés, et ils sont venus à toi, Je vis, moi, dit le Seigneur: de tous ceux-ci, comme d’un ornement, tu seras revêtue, et tu t’en pareras comme une épouse.
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
Tes déserts et tes solitudes, et ta terre ruinée seront maintenant étroits eu égard aux habitants, et ils seront mis en fuite au loin, ceux qui te dévoraient.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
Ils te diront encore à tes oreilles, les fils de ta stérilité: Le lieu est étroit; fais-moi de l’espace, afin que j’habite.
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
Et tu diras dans ton cœur: Qui m’a engendré ceux-ci? j’étais stérile, et je n’enfantais pas; exilée et captive; et ceux-ci, qui les a nourris? j’étais abandonnée et seule, et ceux-ci, où étaient-ils?
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voici que vers des nations j’élèverai ma main, et devant des peuples je hausserai mon étendard; et ils apporteront tes fils entre leurs bras, et tes filles, ils les porteront sur leurs épaules.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
Et les rois seront tes nourriciers, et les reines tes nourrices; la face contre terre, ils se prosterneront devant toi, et ils lécheront la poussière de tes pieds. Et tu sauras que je suis le Seigneur, dans lequel ne seront pas confondus ceux qui l’attendent.
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Est-ce qu’on ôtera à un homme fort sa proie? ou ce qui a été pris par un homme robuste, pourra-t-il être sauvé?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
Parce que voici ce que dit le Seigneur: Certainement et les captifs seront ôtés à un homme fort, et ce qui aura été enlevé par un homme robuste sera sauvé. Or ceux qui t’ont jugée, moi je les jugerai, et tes fils, moi je les sauverai.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Et je nourrirai tes ennemis de leurs propres chairs, et comme d’un vin nouveau je les enivrerai de leur sang; et toute chair saura que c’est moi le Seigneur qui te sauve, et que ton rédempteur est le fort de Jacob.

< Ishaya 49 >