< Ishaya 49 >

1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Ecoutes-moi, Iles, et soyez attentifs, vous peuples éloignés; l'Eternel m'a appelé dès le ventre; il a fait mention de mon nom dès les entrailles de ma mère.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
Et il a rendu ma bouche semblable à une épée aiguë; il m'a caché dans l'ombre de sa main, et m'a rendu semblable à une flèche bien polie, il m'a serré dans son carquois.
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
Et il m'a dit; tu es mon serviteur; Israël [est] celui en qui je me glorifierai par toi.
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
Et moi j'ai dit; j'ai travaillé en vain; j'ai usé ma force pour néant et sans fruit; toutefois mon droit est par-devers l'Eternel, mon œuvre est par-devers mon Dieu.
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
Maintenant donc l'Eternel, qui m'a formé dès le ventre pour lui être serviteur, m'a dit que je lui ramène Jacob; mais Israël ne se rassemble point; toutefois je serai glorifié aux yeux de l'Eternel, et mon Dieu sera ma force.
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
Et il m'a dit; c'est peu de chose que tu me sois serviteur pour rétablir les Tribus de Jacob, et pour délivrer les captifs d'Israël; c'est pourquoi je t'ai donné pour lumière aux nations, afin que tu sois mon salut jusques au bout de la terre.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Ainsi a dit l'Eternel, le Rédempteur, le Saint d'Israël, à la personne méprisée, à celui qui est abominable dans la nation, au serviteur de ceux qui dominent; les Rois le verront, et se lèveront, et les principaux aussi, et ils se prosterneront [devant lui], pour l'amour de l'Eternel, qui [est] fidèle, [et] du Saint d'Israël qui t'a élu.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Ainsi a dit l'Eternel; je t'ai exaucé au temps de la bienveillance, et je t'ai aidé au jour du salut; je te garderai, et je te donnerai pour être l'alliance du peuple, pour rétablir la terre, et afin que tu possèdes les héritages désolés.
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
Disant à ceux qui sont garrottés; sortez; et à ceux qui sont dans les ténèbres; montrez-vous. Ils paîtront sur les chemins, et leurs pâturages seront sur tous les lieux haut élevés.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
Ils n'auront point de faim; ils n'auront point de soif; et la chaleur, ni le soleil ne les frappera plus, car celui qui a pitié d'eux les conduira, et les mènera aux sources d'eaux.
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
Et je réduirai toutes mes montagnes en chemins, et mes sentiers seront relevés.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Voici, ceux-ci viendront de loin; et voici, ceux-là viendront de l'Aquilon, et [ceux-là] de la mer, et les autres du pays des Siniens.
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
O cieux! réjouissez-vous avec chant de triomphe, et toi terre, égaye-toi, et vous montagnes, éclatez de joie avec chant de triomphe; car l'Eternel a consolé son peuple, et il aura compassion de ceux qu'il aura affligés.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Mais Sion a dit; l'Eternel m'a délaissée, et le Seigneur m'a oubliée.
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
La femme peut-elle oublier son enfant qu'elle allaite, en sorte qu'elle n'ait point pitié du fils de son ventre? Mais quand les femmes les auraient oubliés, encore ne t'oublierai-je pas, moi
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Voici, je t'ai portraite sur les paumes de mes mains; tes murs sont continuellement devant moi.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Tes enfants viendront à grande hâte; mais ceux qui te détruisaient et qui te réduisaient en désert, sortiront du milieu de toi.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Elève tes yeux à l'environ, et regarde; tous ceux-ci se sont assemblés, ils sont venus à toi. Je suis vivant, dit l'Eternel, que tu te revêtiras de ceux-ci comme d'un ornement, et tu t'en orneras, comme une épouse.
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
Car tes déserts, et tes lieux désolés, et ton pays détruit, sera maintenant trop étroit pour ses habitants, et ceux qui t'engloutissaient s'éloigneront.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
Les enfants que tu auras, après avoir perdu les autres, diront encore, toi l'entendant; ce lieu est trop étroit pour moi, fais-moi place afin que j'y puisse demeurer.
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
Et tu diras en ton cœur; qui m'a engendré ceux-ci; vu que j'avais perdu mes enfants, et que j'étais seule? emmenée en captivité, et agitée, et qui m'a nourri ceux-ci? voici, j'étais demeurée toute seule, et ceux-ci où étaient-ils?
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel; voici, je lèverai ma main vers les nations, et j'élèverai mon enseigne vers les peuples; et ils apporteront tes fils entre leurs bras, et on chargera tes filles sur les épaules.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
Et les Rois seront tes nourriciers, et les Princesses leurs femmes tes nourrices; ils se prosterneront devant toi le visage contre terre, et lécheront la poudre de tes pieds; et tu sauras que je suis l'Eternel, et que ceux qui se confient en moi ne seront point honteux.
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Le pillage sera-t-il ôté à l'homme puissant? et les captifs du juste seront-ils délivrés?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
Car ainsi a dit l'Eternel; même les captifs pris par l'homme puissant, lui seront ôtés, et le pillage de l'homme fort sera enlevé; car je plaiderai moi-même avec ceux qui plaident contre toi, et je délivrerai tes enfants.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Et je ferai que ceux qui t'auront opprimée mangeront leur propre chair, et s'enivreront de leur sang, comme du moût, et toute chair connaîtra que je suis l'Eternel qui te sauve, et ton Rédempteur, le puissant de Jacob.

< Ishaya 49 >