< Ishaya 49 >

1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Écoutez-moi, îles. Écoutez, vous, peuples, de loin: Yahvé m'a appelé depuis le ventre de ma mère; de l'intérieur de ma mère, il a mentionné mon nom.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
Il a rendu ma bouche semblable à une épée tranchante. Il m'a caché dans l'ombre de sa main. Il m'a fait une tige polie. Il m'a gardé près de lui dans son carquois.
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
Il m'a dit: « Tu es mon serviteur, Israël, en qui je serai glorifié. »
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
Mais j'ai dit: « C'est en vain que j'ai travaillé. J'ai dépensé mes forces en vain pour rien; mais c'est à Yahvé que revient la justice qui m'est due, et ma récompense auprès de mon Dieu. »
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
Or, Yahvé, celui qui m'a formé dès le ventre de ma mère pour être son serviteur, dit de lui ramener Jacob, et de rassembler Israël auprès de lui, car je suis honorable aux yeux de Yahvé, et mon Dieu est devenu ma force.
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
En effet, il dit: « C'est une chose trop légère que tu sois mon serviteur pour relever les tribus de Jacob, et de restaurer les préservés d'Israël. Je te donnerai aussi comme lumière aux nations, afin que tu sois mon salut jusqu'au bout du monde. »
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Yahvé, le Rédempteur d'Israël, et son Saint, dit à celui que l'homme méprise, à celui que la nation abhorre, à un serviteur des chefs: « Les rois verront et se lèveront, les princes, et ils se prosterneront, à cause de Yahvé qui est fidèle, le Saint d'Israël, qui t'a choisi. »
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Yahvé dit: « Je t'ai répondu au bon moment. Je vous ai aidé au jour du salut. Je te garderai et te donnerai comme alliance du peuple, pour relever le pays, pour leur faire hériter de l'héritage dévasté,
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
en disant à ceux qui sont liés: « Sortez! »; à ceux qui sont dans les ténèbres: « Montrez-vous! « Ils se nourriront le long des chemins, et leur pâturage sera sur toutes les hauteurs sans arbres.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
Ils n'auront ni faim ni soif; ni la chaleur ni le soleil ne les frapperont, car celui qui a pitié d'eux les conduira. Il les guidera vers des sources d'eau.
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
Je ferai de toutes mes montagnes une route, et mes autoroutes seront exaltées.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Voici, ils viennent de loin, et voici ceux du nord et de l'ouest, et ceux-ci du pays de Sinim. »
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
Chantez, cieux, et soyez joyeux, terre! Laissez-vous aller à chanter, montagnes! Car Yahvé a réconforté son peuple, et aura de la compassion pour ses affligés.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Mais Sion dit: « Yahvé m'a abandonné, et le Seigneur m'a oublié. »
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
« Une femme peut-elle oublier son enfant qu'elle allaite, pour qu'elle n'ait pas de compassion pour le fils de ses entrailles? Oui, ils peuvent oublier, mais je ne vous oublierai pas!
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Voici, je vous ai gravés sur les paumes de mes mains. Vos murs sont continuellement devant moi.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Vos enfants se dépêchent. Vos destructeurs et ceux qui vous ont dévasté vous quitteront.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Lève les yeux tout autour, et regarde: tous ceux-là se rassemblent et viennent à toi. Je suis vivant, dit Yahvé, et tu t'en revêtiras comme d'une parure, et habille-toi avec, comme une mariée.
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
« En effet, pour ce qui est de tes déchets et de tes lieux désolés, et votre terre qui a été détruite, Il est certain que maintenant cette terre sera trop petite pour les habitants, et ceux qui t'ont englouti seront loin.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
Les enfants de ton deuil diront à tes oreilles, Cet endroit est trop petit pour moi. Donnez-moi un endroit où vivre.
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
Alors tu diras dans ton cœur: « Qui les a conçus pour moi, puisque je suis privé de mes enfants? et que je suis seul, exilé, et que j'erre de long en large? Qui les a évoqués? Voici, j'ai été laissé seul. Où étaient-ils? »
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
Le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je lève ma main vers les nations, et je lèverai ma bannière vers les peuples. Ils porteront vos fils dans leur sein, et vos filles seront portées sur leurs épaules.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
Les rois seront vos pères nourriciers, et leurs reines vos mères nourricières. Ils se prosterneront devant toi, le visage tourné vers la terre, et lécher la poussière de vos pieds. Alors vous saurez que je suis Yahvé; et ceux qui m'attendent ne seront pas déçus. »
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Le butin sera pris aux puissants, ou que les captifs légitimes soient délivrés?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
Mais Yahvé dit: « Même les captifs des puissants seront emmenés, et le butin récupéré sur le féroce, car je me battrai avec celui qui se battra avec vous. et je sauverai vos enfants.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Je nourrirai de leur propre chair ceux qui vous oppriment; et ils s'enivreront de leur propre sang, comme d'un vin doux. Alors toute chair saura que moi, Yahvé, je suis votre Sauveur. et ton rédempteur, le Puissant de Jacob. »

< Ishaya 49 >