< Ishaya 49 >
1 Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
Hearken, O isles, unto me; and listen, ye people, from afar: The Lord hath called me from my birth; from my mother's womb hath he made mention of my name.
2 Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
And he hath rendered my mouth like a sharp sword; in the shadow of his hand hath he hidden me: and he hath rendered me as a polished arrow; in his quiver hath he concealed me;
3 Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
And said unto me, My servant art thou, O Israel, thou on whom I will be glorified.
4 Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
But I had indeed said, For no purpose have I labored, for naught and vanity have I spent my strength; yet surely my cause is with the Lord, and the recompense of my work with my God.
5 Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
And now hath said the Lord that formed me from the womb to be his servant, to bring Jacob again to him, that Israel may be gathered unto him, that I should be honored in the eyes of the Lord, while my God was my strength, —
6 ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
And he said, It is too light a thing that thou shouldst be my servant to raise up the tribes of Jacob, and to bring back the preserved of Israel! but I will [also] appoint thee for a light to the nations, that my salvation may reach as far as the end of the earth.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
Thus hath said the Lord, the Redeemer of Israel, his Holy One, to him who is despised by men, to him who is abhorred by nations, to the servant of rulers, Kings shall see it and rise up, princes, and they shall prostrate themselves, for the sake of the Lord, who is faithful, the Holy One of Israel, who hath made choice of thee.
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
Thus hath said the Lord, In the time of favor have I answered thee, and on the day of salvation have I helped thee; and I will preserve thee, and I will appoint thee as a people of my covenant to raise up the land, to divide out desolate heritages;
9 don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
When I say to the prisoners, Go forth; to those that are in darkness, Show yourselves. On the roads shall they feed, and on all mountain-peaks shall be their pasture.
10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
They shall not be hungry nor thirsty, and neither heat nor sun shall smite them; for he that hath mercy on them will lead them, and by springs of water will he guide them.
11 Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
And I will change all my mountains into a road, and my highways shall be lifted up.
12 Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
Behold, these shall come from afar; and, lo, these from the north and from the west; and these from the land of Sinim.
13 Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
Sing, O heavens; and be joyful, O earth; and break forth, O mountains, into song; for the Lord hath comforted his people, and upon his oppressed will he have mercy.
14 Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
Yet Zion said, the Eternal hath forsaken me, and the Lord hath forgotten me.
15 “Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
Can a woman forget her sucking child, not to have mercy on the son of her body? yea, should these even forget, yet would I not forget thee.
16 Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
Behold, upon the palms of my hands have I engraved thee; thy walls are continually before me.
17 ’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
Thy children come in haste; thy destroyers and they that laid thee waste shall go away from thee.
18 Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
Lift up thy eyes round about, and see; they all are assembled together, they come to thee: as I live, saith the Lord, thou shalt surely clothe thyself with them all, as with an ornament, and bind them on thee, as a bride.
19 “Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
For thy ruins and thy desolate places, and thy wasted land, —yea, now shall it be too narrow for thee by reason of the inhabitants, and thy destroyers shall be far away.
20 ’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
Yet again will say before thy ears the children of whom thou wast deprived, The place is too narrow for me; make room for me that I may dwell.
21 Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
And thou wilt say in thy heart, Who hath born me these, seeing I was bereft of my children, and was solitary, an exile, and outcast? and who hath brought up these? Behold, I was left entirely alone; these, where have they been?
22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will lift up to the nations my hand, and to the people will I raise up high my standard; and they shall bring thy sons in [their] arms, and thy daughters shall be carried upon shoulders.
23 Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
And kings shall be thy nursing-fathers, and their princesses thy nursing-mothers; with the face toward the earth shall they bow down to thee, and the dust of thy feet shall they lick up: and thou shalt know that I am the Lord, who will not suffer those who hope in me to be ashamed.
24 Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
Shall the prey be taken from the mighty, or shall the captive of the victor escape?
25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
For thus hath said the Lord, Also the captive of the mighty shall be taken away, and the prey of the powerful shall escape; and with those who contend against thee will I contend, and thy children will I indeed save.
26 Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
And I will feed thy oppressors with their own flesh; and as with new wine shall they be made drunken with their own blood: and all flesh shall know that I the Eternal am thy Saviour, and thy Redeemer the Mighty One of Jacob.