< Ishaya 48 >
1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Hören detta, I av Jakobs hus, I som ären uppkallade med Israels namn och flutna ur Juda källa, I som svärjen vid HERRENS namn och prisen Israels Gud -- dock icke i sanning och rättfärdighet,
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
allt medan I kallen eder efter den heliga staden och stödjen eder på Israels Gud, på honom vilkens namn är HERREN Sebaot.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
Vad förut skedde, det hade jag för länge sedan förkunnat; av min mun var det förutsagt, och jag hade låtit eder höra därom. Plötsligt satte jag det i verket, och det inträffade.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Eftersom jag visste, att du var så styvsint, ja, att din nacksena var av järn och din panna av koppar,
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
därför förkunnade jag det för länge sedan och lät dig höra därom, innan det skedde, på det att du icke skulle kunna säga: "Min gudastod har gjort det, min gudabild, den skurna eller den gjutna har skickat det så."
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Du hade hört det, nu kan du se alltsammans; viljen I då icke erkänna det? Nu låter jag dig åter höra om nya ting, om fördolda ting som du ej har vetat av.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
Först nu hava de blivit skapade, icke tidigare, och förrän i dag fick du icke höra om dem, på det att du ej skulle kunna säga: "Det visste jag ju förut."
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Du fick icke förr höra något därom eller veta något därav, ej heller kom det tidigare för dina öron, eftersom jag visste, huru trolös du var och att du hette "överträdare" allt ifrån moderlivet.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
Men för mitt namns skull är jag långmodig, och för min äras skull håller jag tillbaka min vrede, så att du icke bliver utrotad.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Se, jag har smält dig, men silver har jag icke fått; jag har prövat dig i lidandets ugn.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
För min egen skull, ja, för min egen skull gör jag så, ty huru skulle jag kunna låta mitt namn bliva ohelgat? Jag giver icke min ära åt någon annan.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Hör på mig, du Jakob, du Israel, som jag har kallat. Jag är det; jag är den förste, jag är ock den siste.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Min hand har lagt jordens grund, och min högra hand har utspänt himmelen; jag kallar på dem, då stå de där båda.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Församlen eder, I alla, och hören: Vem bland dessa andra har förutsagt detta, att den man, som HERREN älskar, skall utföra hans vilja mot Babel och vara hans arm mot kaldéerna?
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
Jag, jag har talat detta, jag har ock kallat honom, jag har fört honom fram, så att hans väg har blivit lyckosam.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Träden hit till mig och hören detta; Mina förutsägelser har jag icke talat i det fördolda; när tiden kom, att något skulle ske, då var jag där. Och nu har Herren, HERREN sänt mig och sänt sin Ande.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Så säger HERREN, din förlossare, Israels Helige: Jag är HERREN, din Gud, den som lär dig, vad nyttigt är, den som leder dig på den väg du skall vandra.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
O att du ville akta på mina bud! Då skulle frid tillflyta dig såsom en ström och din rätt såsom havets böljor;
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
dina barn skulle då vara såsom sanden och din livsfrukt såsom sandkornen, dess namn skulle aldrig bliva utrotat eller utplånat ur min åsyn.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Dragen ut från Babel, flyn ifrån kaldéernas land; förkunnen det med fröjderop och låten det bliva känt, utbreden ryktet därom till jordens ända; sägen: "HERREN har förlossat sin tjänare Jakob."
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
De ledo ingen törst, när han förde dem genom ödemarker, ty han lät vatten strömma fram ur klippan åt dem, han klöv sönder klippan, och vattnet flödade.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
Men de ogudaktiga få ingen frid, säger HERREN.