< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
ای قوم اسرائیل، ای کسانی که از نسل یهودا هستید، گوش کنید: شما به نام خداوند قسم می‌خورید و ادعا می‌کنید که خدای اسرائیل را می‌پرستید، اما این کار را از روی صداقت و راستی انجام نمی‌دهید.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
با وجود این، افتخار می‌کنید که در شهر مقدّس زندگی می‌کنید و بر خدای اسرائیل که نامش خداوند لشکرهای آسمان است توکل دارید.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
خداوند می‌گوید: «آنچه را که می‌بایست رخ دهد، از مدتها پیش به شما اطلاع دادم؛ سپس به‌ناگاه آنها را به عمل آوردم.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
می‌دانستم که دلهایتان همچون سنگ و سرهایتان مانند آهن سخت است.
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
این بود که آنچه می‌خواستم برای شما انجام دهم از مدتها پیش به شما خبر دادم تا نگویید که بتهایتان آنها را بجا آورده‌اند.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
«پیشگویی‌های مرا شنیده‌اید و وقوع آنها را دیده‌اید، اما نمی‌خواهید اعتراف کنید که پیشگویی‌های من درست بوده است. اکنون چیزهای تازه‌ای می‌گویم که تا به حال از وجود آنها بی‌اطلاع بوده‌اید.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
و چیزهایی را به وجود می‌آورم که پیش از این نبوده است و دربارهٔ آنها چیزی نشنیده‌اید، تا دیگر نگویید:”این چیزها را می‌دانستیم!“
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
«بله، چیزهای کاملاً تازه به شما می‌گویم، چیزهایی که هرگز نشنیده‌اید، چون می‌دانم اشخاص خیانتکاری هستید و از طفولیت همیشه یاغی بوده‌اید.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
با وجود این، به خاطر حرمت نامم، خشم خود را فرو برده، شما را از بین نخواهم برد.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
شما را تصفیۀ کردم، اما نه مانند نقره؛ شما را در کورۀ مصیبت تصفیه کردم.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
بله، به خاطر خودم شما را از بین نخواهم برد مبادا اقوام بت‌پرست بگویند که بتهایشان مرا مغلوب کردند. من به بتهای آنها اجازه نمی‌دهم در جلال من شریک شوند.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
«ای اسرائیل، ای قوم برگزیدهٔ من، گوش کنید! تنها من خدا هستم. من اول و آخر هستم.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
دستهای من بود که زمین را بنیاد نهاد و آسمانها را گسترانید. آنها گوش به فرمان من هستند.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
«همهٔ شما بیایید و بشنوید. هیچ‌کدام از خدایان شما قادر نیست پیشگویی کند که مردی را که من برگزیده‌ام حکومت بابِل را سرنگون خواهد کرد و آنچه اراده کرده‌ام بجا خواهد آورد.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
اما من این را پیشگویی می‌کنم. بله، من کوروش را خوانده‌ام و به او این مأموریت را داده‌ام و او را کامیاب خواهم ساخت.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
«به من نزدیک شوید و گوش دهید. من همیشه آشکارا گفته‌ام که در آینده چه رخ خواهد داد تا شما بتوانید آن را بفهمید.» (اکنون خداوند یهوه مرا با روح خود نزد شما فرستاده است.)
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
خداوند که نجا‌ت‌دهندۀ قوم اسرائیل و خدای قدوس ایشان است چنین می‌گوید: «ای اسرائیل، من یهوه، خدای تو هستم، که آنچه برای تو نیکوست، آن را به تو تعلیم می‌دهم و تو را به راههایی که باید بروی هدایت می‌کنم.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
«ای کاش به اوامر من گوش می‌دادید، آنگاه برکات مانند نهر برای شما جاری می‌شد و پیروزی مانند امواج دریا به شما می‌رسید.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
نسل شما مانند شنهای ساحل دریا بی‌شمار می‌شدند و من نمی‌گذاشتم ایشان هلاک شوند.»
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
ای قوم اسرائیل، از بابِل بیرون بیایید! از اسارت آزاد شوید! با صدای بلند سرود بخوانید و این پیام را به گوش تمام مردم جهان برسانید: «خداوند قوم اسرائیل را که خدمتگزاران او هستند، آزاد ساخته است!»
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
هنگامی که خداوند قوم خود را از بیابان خشک عبور داد ایشان تشنگی نکشیدند، زیرا او صخره را شکافت و از آن، آب جاری ساخت تا ایشان بنوشند.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
خداوند می‌فرماید: «شریران از سلامتی برخوردار نخواهند شد.»

< Ishaya 48 >