< Ishaya 48 >
1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Ecoutez ceci, maison de Jacob, vous qui êtes appelés du nom d’Israël, et êtes sortis des eaux de Juda, qui jurez au nom du Seigneur, qui vous souvenez du Dieu d’Israël, mais non dans la vérité et la justice.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
Car ils ont été appelés du nom de la cité sainte, et sur le Dieu d’Israël ils se sont appuyés; le Seigneur des armées est son nom.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
J’ai annoncé dès lors les événements passés; c’est de ma bouche qu’ils sont sortis et je les ai fait entendre; je les ai accomplis tout d’un coup, et ils sont arrivés.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Car je savais que tu es dur, que ton cou est une chaîne de fer, et ton front d’airain.
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
Je t’ai prédit dès lors ces choses; avant qu’elles vinssent je te les ai indiquées, de peur que tu ne dises: Ce sont mes idoles qui les ont faites, et mes images taillées au ciseau et jetées en fonte qui les ont ordonnées.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Les choses que tu as entendues, vois-les toutes; mais vous, est-ce que vous les avez annoncées? Je t’en ai fait entendre dès lors de nouvelles; et il en est de réservées que tu ne connais pas;
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
C’est maintenant qu’elles ont été créées, et non pas alors; avant un jour seulement, et tu ne les as pas entendues, de peur que tu ne dises: Voici que moi je les connaissais.
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Tu n’as entendu, ni connu, ton oreille même alors n’était pas ouverte; car je sais que prévariquant, tu prévariqueras, et je t’ai appelé transgresseur dès le sein de ta mère.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
À cause de mon nom, j’éloignerai ma fureur, et pour ma gloire je te mettrai un frein, pour que tu ne périsses pas,
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Je t’ai purifié par le feu, mais non comme l’argent: j’ai choisi pour toi le fourneau de la pauvreté.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
C’est à cause de moi, à cause de moi que je ferai que mon nom ne soit pas blasphémé, et je ne donnerai pas ma gloire à un autre.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Ecoute-moi, Jacob, et toi, Israël, que j’appelle; moi qui suis, moi le premier, et moi le dernier.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Ma main aussi a fondé la terre, et ma droite a étendu les cieux; moi, je les appellerai, et ils seront là tous ensemble.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Rassemblez-vous tous et écoutez-moi: qui d’entre eux a annoncé ces choses? Le Seigneur l’a aimé, il fera sa volonté dans Babylone; et il sera son bras parmi les Chaldéens.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
C’est moi, c’est moi qui ai parlé, et je l’ai appelé; je l’ai amené, et sa voie est aplanie.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Approchez-vous de moi, et écoutez ceci: dès le principe je n’ai pas parlé en secret; dans le temps même, avant l’événement, j’étais là; et maintenant le Seigneur et son esprit m’ont envoyé.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Voici ce que dit le Seigneur ton rédempteur, le saint d’Israël: Moi le Seigneur ton Dieu, je t’enseigne des choses utiles, je te dirige dans la voie par laquelle tu marches.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
Oh! si tu avais été attentif à mes commandements, ta paix aurait été comme un fleuve, et ta justice comme les flots de la mer;
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Ta postérité eût été comme le sable de ses rivages, et les rejetons de ton sein comme les petites pierres de ses bords; le nom de la race n’aurait pas péri, et il n’eût pas été effacé de devant ma face.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Sortez de Babylone, fuyez de chez les Chaldéens, avec la voix de l’exultation annoncez cette nouvelle, faites-la entendre et portez-la jusqu’aux extrémités de la terre. Dites: Le Seigneur a racheté son serviteur Jacob.
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
Ils n’ont pas eu soif dans le désert, lorsqu’il les ramenait; il fit sortir de l’eau d’une pierre pour eux, et il fendit la pierre et des eaux coulèrent.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
Il n’y a point de paix pour les impies, dit le Seigneur.