< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Ecoutez ceci, maison de Jacob, qui êtes appelés du nom d'Israël, et qui êtes issus des eaux de Juda, qui jurez par le nom de l'Eternel, et qui faites mention du Dieu d'Israël, mais non pas conformément à la vérité, et à la justice.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
Car ils prennent leur nom de la sainte Cité, et s'appuient sur le Dieu d'Israël, duquel le nom est l'Eternel des armées.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
J'ai déclaré dès jadis les choses qui ont précédé, et elles sont sorties de ma bouche, et je les ai publiées; je les ai faites subitement, et elles sont arrivées.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Parce que j'ai connu que tu étais revêche, et que ton cou était [comme une] barre de fer, et que ton front était d'airain;
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
Je t'ai déclaré ces choses dès lors, et je te les ai fait entendre avant qu'elles arrivassent, de peur que tu ne disses; mes dieux ont fait ces choses, et mon image taillée, et mon image de fonte les ont commandées.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Tu l'as ouï, vois tout ceci; et vous, ne l'annoncerez-vous pas? je te fais entendre dès maintenant des choses nouvelles, et qui étaient en réserve, et que tu ne savais pas.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
Maintenant elles ont été créées, et non pas dès jadis, et avant ce jour-ci tu n'en avais rien entendu, afin que tu ne dises pas; voici, je les savais bien.
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Encore n'as-tu pas entendu; encore n'as-tu pas connu, et depuis ce temps ton oreille n'a point été ouverte; car j'ai connu que tu agirais perfidement; aussi as-tu été appelé Transgresseur dès le ventre.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
Pour l'amour de mon Nom je différerai ma colère, et pour l'amour de ma louange je retiendrai mon courroux contre toi, afin de ne te retrancher pas.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Voici, je t'ai épuré, mais non pas comme [on épure] l'argent; je t'ai élu au creuset de l'affliction.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
Pour l'amour de moi, pour l'amour de moi je le ferai; car comment [mon Nom] serait-il profané? certes je ne donnerai point ma gloire à un autre
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Ecoute-moi, Jacob, et toi Israël, appelé par moi; c'est moi qui suis le premier, et qui suis aussi le dernier.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Ma main aussi a fondé la terre, et ma droite a mesuré les cieux à l'empan; quand je le les appelle, ils comparaissent ensemble.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Vous tous, assemblez-vous, et écoutez; lequel de ceux-là a déclaré de telles choses? l'Eternel l'a aimé, il mettra en exécution son bon plaisir contre Babylone, et son bras sera contre les Chaldéens.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
C'est moi, c'est moi qui ai parlé, je l'ai aussi appelé, je l'ai amené, et ses desseins lui ont réussi.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Approchez-vous de moi, et écoutez ceci; dès le commencement je n'ai point parlé en secret, au temps que la chose a été faite, j'ai été là. Or maintenant le Seigneur l'Eternel, et son Esprit, m'ont envoyé.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Ainsi a dit l'Eternel ton Rédempteur, le Saint d'Israël; je suis l'Eternel ton Dieu, qui t'enseigne à profiter, et qui te guide par le chemin où tu dois marcher.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
O si tu eusses été attentif à mes commandements! car ta paix eût été comme un fleuve, et ta justice comme les flots de la mer.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Et ta postérité eût été [multipliée] comme le sable, et ceux qui sortent de tes entrailles, comme le gravier de la mer; son nom n'eût point été retranché ni effacé de devant ma face.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Sortez de Bapylone, fuyez loin des Chaldéens; publiez ceci avec une voix de chant de triomphe, annoncez, publiez ceci, et le mandez dire jusques au bout de la terre; dites, l'Eternel a racheté son serviteur Jacob.
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
Et ils n'ont point eu soif quand il les a fait marcher par les déserts; il leur a fait découler l'eau hors du rocher, même il leur a fendu le rocher, et les eaux en sont découlées.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
Il n'y a point de paix pour les méchants, a dit l'Eternel.

< Ishaya 48 >