< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Écoutez ceci, maison de Jacob, vous qui êtes appelés du nom d’Israël et qui sortez des eaux de Juda, qui jurez par le nom de l’Éternel, et faites mention du Dieu d’Israël, [mais] non pas en vérité ni en justice.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
Car ils se nomment d’après la ville sainte, et s’appuient sur le Dieu d’Israël: l’Éternel des armées est son nom.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
J’ai déclaré les premières choses dès longtemps, et elles sont sorties de ma bouche et je les ai fait entendre; je les ai faites subitement, et elles sont arrivées.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Parce que je savais que tu es obstiné, et que ton cou est une barre de fer, et ton front, d’airain,
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
je te les ai déclarées dès longtemps; avant qu’elles arrivent je te les ai fait entendre, de peur que tu ne dises: Mon idole les a faites; et mon image taillée ou mon image de fonte les a ordonnées.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Tu les as entendues, vois-les tout entières. Et vous, ne voulez-vous pas les déclarer? Je t’ai fait entendre des choses nouvelles, dès maintenant, et des choses cachées et que tu n’as pas connues.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
Elles sont créées maintenant, et non dès longtemps; et avant ce jour tu ne les as pas entendues, de peur que tu ne dises: Voici, je les savais!
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Et tu n’as pas entendu, et tu n’as pas su, et dès longtemps ton oreille ne s’est pas ouverte; car je [te] connais: tu agis toujours perfidement, et tu as été appelé transgresseur dès la matrice.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
À cause de mon nom je différerai ma colère, et à cause de ma louange je me retiendrai à ton égard, pour ne pas te retrancher.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Voici, je te purifierai, mais non comme de l’argent: je t’ai choisi au creuset de l’affliction.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
À cause de moi-même, à cause de moi-même, je [le] ferai; car comment [mon nom] serait-il profané? Et je ne donnerai pas ma gloire à un autre.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Écoute-moi, Jacob, et toi, Israël, que j’ai appelé. Moi, je suis le Même, – moi, le premier, et moi, le dernier.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Ma main aussi a fondé la terre, et ma droite a étendu les cieux; moi je les appelle: ils se tiennent là ensemble.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Rassemblez-vous, vous tous, et écoutez. Qui d’entre eux a déclaré ces choses? Celui que l’Éternel a aimé exécutera son bon plaisir sur Babylone, et son bras [sera sur] les Chaldéens.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
Moi, moi j’ai parlé, moi je l’ai aussi appelé; je l’ai fait venir, et son chemin prospérera.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Approchez-vous de moi, écoutez ceci: Je n’ai pas parlé en secret dès le commencement; dès le temps où cela a existé, je suis là; et maintenant le Seigneur l’Éternel m’a envoyé, et son Esprit.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Ainsi dit l’Éternel, ton rédempteur, le Saint d’Israël: Moi, je suis l’Éternel, ton Dieu, qui t’enseigne pour ton profit, qui te dirige dans le chemin [par lequel] tu dois marcher.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
Oh! si tu avais fait attention à mes commandements, ta paix aurait été comme un fleuve, et ta justice comme les flots de la mer;
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
et ta semence aurait été comme le sable, et ceux qui sortent de tes entrailles, comme le gravier de la mer: son nom n’aurait pas été retranché ni détruit de devant moi.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Sortez de Babylone, fuyez du milieu des Chaldéens, avec une voix de chant de joie! Déclarez et faites entendre ceci, portez-le jusqu’au bout de la terre; dites: L’Éternel a racheté son serviteur Jacob!
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
Et ils n’ont pas eu soif, quand il les fit marcher dans les déserts; du rocher il a fait jaillir pour eux les eaux; il a fendu le rocher, et les eaux ont coulé.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
Il n’y a pas de paix, dit l’Éternel, pour les méchants.

< Ishaya 48 >