< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
« Écoutez ceci, maison de Jacob, vous qui êtes appelés par le nom d'Israël, et sont sortis des eaux de Judée. Vous jurez par le nom de Yahvé, et faire mention du Dieu d'Israël, mais pas dans la vérité, ni dans la droiture-
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
car ils se disent citoyens de la ville sainte, et s'en remettre au Dieu d'Israël; Yahvé des Armées est son nom.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
J'ai annoncé les choses anciennes dès les temps anciens. Oui, ils sont sortis de ma bouche, et je les ai révélés. Je les ai fait soudainement, et ils sont arrivés.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Car je savais que tu étais obstiné, et ton cou est un tendon de fer, et ton front bronze;
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
C'est pourquoi je vous l'ai annoncé dès le début; avant que cela ne se produise, je vous l'ai montré; de peur que vous ne disiez: « C'est mon idole qui les a faites ». Mon image gravée et mon image fondue leur a commandé.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Vous l'avez entendu. Maintenant, voyez tout ça. Et vous, ne le déclarerez-vous pas? « Je vous ai montré des choses nouvelles depuis ce temps, même des choses cachées, que vous n'avez pas connues.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
Ils sont créés maintenant, et non pas d'autrefois. Avant aujourd'hui, tu ne les entendais pas, de peur que tu ne dises: « Voici, je les connaissais.
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Oui, vous n'avez pas entendu. Oui, vous ne saviez pas. Oui, depuis longtemps, ton oreille n'a pas été ouverte, car je savais que tu étais très déloyal, et tu as été appelé transgresseur dès le ventre de ta mère.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
Pour l'amour de mon nom, je retarderai ma colère, et pour mon éloge, je le retiens pour vous pour que je ne vous coupe pas la route.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Voici, je vous ai raffiné, mais pas en argent. Je t'ai choisi dans la fournaise de l'affliction.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
Pour mon propre bien, pour mon propre bien, je le ferai; car comment mon nom serait-il profané? Je ne donnerai pas ma gloire à un autre.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
« Écoute-moi, ô Jacob! et Israël mon appelé: Je suis lui. Je suis le premier. Je suis aussi le dernier.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Oui, ma main a posé les fondements de la terre, et ma main droite a déployé les cieux. quand je les appelle, ils se lèvent ensemble.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
« Assemblez-vous, vous tous, et écoutez! Qui parmi eux a déclaré ces choses? Celui que Yahvé aime fera ce qu'il aime à Babylone, et son bras sera contre les Chaldéens.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
C'est moi, moi aussi, qui ai parlé. Oui, je l'ai appelé. Je l'ai amené et il fera prospérer son chemin.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
« Approche-toi de moi et écoute ceci: « Dès le début, je n'ai pas parlé en secret; à partir du moment où c'est arrivé, j'étais là. » Le Seigneur Yahvé m'a envoyé avec son Esprit.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Yahvé, votre Rédempteur, le Saint d'Israël, dit: « Je suis Yahvé votre Dieu, qui vous apprend à faire du profit, qui vous conduit par le chemin que vous devez suivre.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
Oh, si vous aviez écouté mes commandements! Alors ta paix aurait été comme une rivière et ta justice comme les vagues de la mer.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Ta descendance aurait été comme le sable. et les descendants de ton corps comme ses grains. Son nom ne sera pas retranché ni détruit devant moi. »
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Quittez Babylone! Fuyez les Chaldéens! Avec une voix chantante, annoncez ceci, le raconter jusqu'au bout du monde; dire: « Yahvé a racheté son serviteur Jacob! »
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
Ils n'ont pas eu soif quand il les a conduits à travers les déserts. Il a fait jaillir les eaux du rocher pour eux. Il a aussi fendu le rocher et les eaux ont jailli.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
« Il n'y a pas de paix », dit Yahvé, « pour les méchants ».

< Ishaya 48 >