< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
[Yahweh says], “You descendants [MTY] of Jacob, who are [also] descendants of Judah and are now called [the people of] Israel, Listen to me! You make solemn promises using my name, Yahweh, and you request that I, the God to whom you Israeli people belong, [will hear you], but you do not do it sincerely.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
You say that you live in the holy city [of Jerusalem], and [you insincerely say] that you are relying on me, the God to whom you [people of] Israel belong, the one who is the Commander of the armies of angels.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
Long ago I [MTY] predicted what would happen [DOU]. And then suddenly, I caused those things to happen.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
I knew that you people are very stubborn; I knew that your heads are [MET] [as hard as] iron or brass [DOU].
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
That is why I told you those things long ago. Long before they occurred, I announced that they would occur, in order that [when they happened] you could not say ‘Our idols did it; our statue made of wood and our idol made of metal caused them to happen.’
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
You have heard those things [that I predicted] and now you have seen that they have all occurred, so why do you not admit it [RHQ]? Now I will tell you new things, things that you have not known previously.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
I am causing them to happen now; they are not things I did long ago. So you cannot say, ‘We already knew about those things.’
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
[I will tell you about] things that you have never heard about or understood before. Even long ago you did not pay attention to me [IDM]. I know that you act very deceitfully/treacherously; you have rebelled against me since you first became a nation [MTY].
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
But, for my own sake, in order that I will be honored, I will not punish [MTY] you immediately and I will not completely get rid of you.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
I have purified you, but not the way [people refine] silver. Instead, I have caused you to suffer very much [to get rid of your impure behavior], like [MET] [people put metal in a very hot] furnace [to get rid of the impurities].
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
But for my [MTY] own sake I will delay punishing you more; I will do it for my own sake in order that my reputation will not be damaged [RHQ]. I will not allow any [person or any idol] to be honored as I [deserve to be] honored.”
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
“You descendants [MTY] of Jacob, you people of Israel whom I have chosen, listen to me! [Only] I am God; I am the one who begins everything and who causes everything to end.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
I [SYN] am the one who laid the foundation of the earth. I stretched out the sky with my hand. And when I tell [the stars] to appear, they all do what I tell them.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
All of you, gather together and listen to me. None of your idols has [RHQ] told this to you: I, Yahweh, have chosen [Cyrus] to assist me, and he will do to Babylon what I want him to do, and his army will get rid of [the army of] Babylonia.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
I have said it; I have summoned [Cyrus]. I have appointed him, and he will accomplish everything that he attempts to do.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Come close to me and listen to what I say. Long ago [MTY] I told you plainly/clearly [LIT] [what would happen], and when those things occurred, I was [causing them to happen].” And now Yahweh the Lord and his Spirit have sent me [to give you a message].
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
This is what Yahweh, the one who saves you, the Holy God of [us] Israelis, says: “I am Yahweh, your God; I teach you what is important for you [to know]; I direct you and lead you to the roads that you should walk on [MET].
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
I wish that you had paid attention to my commands! If you had done that, things would have gone well for you like [SIM] a river that flows gently; you would have been successful again and again, like [SIM] waves that come without ceasing.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Your descendants would have been [as many as] [MET] the grains of sand [on the seashore] [which no one can count]. I would not have needed to get rid of you; the country of [MTY] [Israel] would not have been destroyed.”
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
[However, now I tell you], leave Babylon! Flee from [being slaves of the people of] Babylonia! Proclaim this message joyfully; send it to the most remote/distant places on the earth: Yahweh freed the people of Israel [from being slaves in Egypt].
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
They were not thirsty when he led them through the desert, because he split open the rock and caused water to gush/flow out for them [to drink].
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
“But things will not go well [like that] for wicked people,” says Yahweh.

< Ishaya 48 >