< Ishaya 48 >
1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Hear this, O house of Jacob! Ye that are called by the name of Israel; Ye that have come forth from the fountain of Judah; Ye that swear by the name of Jehovah, And praise the God of Israel, But not in truth and sincerity!
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
For they call themselves of the holy city, And stay themselves on the God of Israel, Whose name is Jehovah of hosts: —
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
What hath happened I declared to you long ago; From my mouth it proceeded, and I made it known; On a sudden I effected it, and it came to pass.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Because I knew that thou art obstinate, And that thy neck is a bar of iron, And that thy brow is brass,
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
I declared it to thee long ago; Before it came to pass, I made it known to thee; Lest thou shouldst say, My idol effected it, And my graven image, and my molten image ordained it.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Thou hast heard it; now see it all! And will ye not confess it? From this time I make you hear a new thing, Even a hidden thing, which thou hast not known.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
It is produced now, and not long ago; Before this day thou hast not heard of it, Lest thou shouldst say, Behold, I knew it.
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Yea, thou heardest it not; yea, thou knewest it not; Yea, it was not disclosed to thee long ago; For I knew that thou wast wholly faithless, And wast called rebellious from thy birth.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
For the sake of my name I will defer my anger, And for the sake of my praise I will restrain it from thee, That I may not utterly cut thee off.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Behold, I have melted thee, and found no silver; I have tried thee in the furnace of affliction.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
For mine own sake will I do it; For how would my name be blasphemed? And my glory will I not give to another.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Hearken to me, O Jacob, And Israel, whom I have called! I am He, I am the first, and I the last.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Yea, my hand hath founded the earth, And my right hand hath spread out the heavens; I called them; they stood forth together.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Assemble yourselves, all of you, and hear! Who among you hath declared these things? He whom Jehovah loveth will execute his pleasure upon Babylon, And his power upon the Chaldaeans.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
I, even I, have spoken; yea, I have called him; I have brought him, and his way shall be prosperous.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Draw near to me, and hear ye this! I spake not in secret from the beginning; And since it began to be, I have been there; And now hath the Lord Jehovah sent me with his spirit.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Thus saith Jehovah, thy Redeemer, the Holy One of Israel; I am Jehovah, thy God, who teacheth thee what will profit thee; Who leadeth thee in the way thou shouldst go.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
O that thou wouldst hearken to my commandments! Then shall thy peace be as a river, And thy prosperity as the waves of the sea;
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Then shall thy posterity be as the sand, And the fruit of thy body as the offspring of the sea; Thy name shall not be cut off, nor destroyed before me.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Come ye forth from Babylon, flee ye from the land of the Chaldaeans with the voice of joy! Publish ye this, and make it known; Let it resound to the ends of the earth! Say: “Jehovah hath redeemed his servant Jacob;
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
They thirst not in the deserts through which he leadeth them; Waters from the rock he causeth to flow for them; He cleaveth the rock, and the waters gush forth.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
There is no peace, saith Jehovah, for the wicked.”