< Ishaya 48 >
1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Hører dette, Jakobs Hus! I, som ere kaldte med Israels Navn, og som ere udgangne af Judas Kilde, I, som sværge Ved Herrens Navn og prise Israels Gud, men ikke i Sandhed og ej i Retfærdighed!
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
Thi de kalde sig efter den hellige Stad og forlade sig fast paa Israels Gud; Herre Zebaoth er hans Navn.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
Jeg har forlængst kundgjort de første Ting, af min Mund ere de udgangne, og jeg lader dem høre det; jeg gør det hastelig, og det sker.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
Efterdi jeg vidste, at du er haard, og din Nakke er Jernsener, og din Pande er Kobber,
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
saa har jeg forlængst kundgjort dig det, jeg lod dig høre det, førend det kom, at du ikke maaske skal sige: Mit Gudebillede gjorde disse Ting, og mit udskaarne Billede og mit støbte Billede beskikkede dem.
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
Hørt det har du, se det nu alt sammen! og I, ville I ikke kundgøre det? jeg har fra nu af ladet dig høre ny Ting, hvad der lønligt var bevaret og hvad du ikke kendte.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
Nu blive de skabte og ikke fra fordums Tid, og før i Dag har du ikke hørt til dem, paa det du ikke skal sige: Se, jeg har kendt dem.
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
Ja, du har ikke hørt det, du vidste det og ikke; ja, dit Øre var heller ikke aabnet fra fordums Tid; thi jeg ved, at du vil handle troløst, og at du er kaldet en Overtræder fra Moders Liv.
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
For mit Navns Skyld vil jeg forhale min Vrede, og for min Æres Skyld holder jeg min Vrede imod dig tilbage, for at jeg ikke skal udrydde dig.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Se, jeg har lutret dig, dog ikke som Sølv; jeg har prøvet dig i Elendigheds Ovn.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
For min Skyld, for min egen Skyld vil jeg gøre det; thi hvorfor skulde mit Navn vanhelliges? og jeg vil ikke give en anden min Ære.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Hør mig, Jakob! og du, Israel, min kaldte! jeg er, jeg er den første, jeg er ogsaa den sidste.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
Ja, min Haand har grundfæstet Jorden, og min højre Haand har udspændt Himlene; jeg kalder dem frem, og de staa der tilsammen.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Samler eder, alle til Hobe, og hører! Hvo iblandt dem har forkyndt disse Ting: Den, Herren elsker, skal gøre efter hans Behag imod Babel og lade hans Arm kendes imod Kaldæerne.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
Jeg, jeg har sagt det, jeg har ogsaa kaldet ham; jeg vil lade ham komme, og hans Vej skal lykkes.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Kommer nær til mig, hører dette! fra Begyndelsen har jeg ikke talt i Løndom; fra den Tid, at det blev til, er jeg der; og nu har den Herre, Herre sendt mig, og sin Aand.
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
Saa siger Herren, din Genløser, Israels Hellige: Jeg er Herren din Gud, som lærer dig, hvad nyttigt er, og som fører dig paa Vejen, som du skal gaa.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
Gid du vilde agte paa mine Bud, da skulde din Fred vorde som Floden og din Retfærdighed som Havets Bølger.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Og din Sæd skulde vorde som Sand, og dit Livs Afkom som dets Smaastene; dens Navn skulde ikke udryddes eller ødelægges for mit Ansigt.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Gaar ud af Babel, flyer fra Kaldæerne; forkynder og lader dette høre med Frydesangs Røst, bringer det ud indtil Jordens Ende, siger: Herren har genløst sin Tjener Jakob.
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
Og de lede ingen Tørst, han ledte dem igennem Ørknerne, han lod flyde Vand af en Klippe til dem; og han kløvede en Klippe, og der flød Vand.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
De ugudelige, siger Herren, have ingen Fred.