< Ishaya 46 >
1 Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
Bel se inclina, Nebo se cae; sus imágenes son puestas sobre las bestias y sobre animales de carga; las cosas que tomaste se han convertido en un peso para la bestia cansada.
2 Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
Están doblados, caen juntos; no pudieron mantener a salvo sus imágenes, pero ellos mismos han sido tomados prisioneros.
3 “Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
Escúchame, oh familia de Jacob, y al resto del pueblo de Israel, que han sido llevados por mi desde desde su nacimiento y cuidado desde la matriz.
4 Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
Incluso cuando seas viejo seré el mismo, y cuando seas canoso te cuidaré; seré responsable de lo que hice; Sí, te llevaré y te mantendré a salvo.
5 “Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
¿Quién en tus ojos es mi igual? ¿O qué comparación harán conmigo?
6 Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
En cuanto a los que sacan el oro de una bolsa y ponen plata en la balanza, dan un pago a un artesano del oro, para convertirlo en un dios; Ellos se bajan sobre sus rostros y le dan adoración.
7 Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
Lo pusieron sobre sus espaldas, lo levantaron y lo pusieron en su lugar fijo, desde donde no puede ser movido; Si un hombre le grita pidiéndole ayuda, no puede dar una respuesta o sacarlo de su apuro.
8 “Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
Tengan esto en mente y tengan vergüenza; Que vuelva a tu memoria, pecadores.
9 Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
Recuerden las cosas pasadas; porque yo soy Dios, y no hay otro; Yo soy Dios, y no hay nadie como yo;
10 Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
Anunciando desde el principio lo que vendrá, y de los tiempos pasados; las cosas que no han sucedido hasta ahora; diciendo: Mis planes son fijos, y haré mi voluntad.
11 Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
Enviando a un pájaro de fuerte vuelo desde el este, el hombre de mi propósito desde un país lejano; Lo he dicho, y le daré efecto; lo planeado por mí ciertamente se hará.
12 Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
Escúchame, duros de corazón, que no tienes fe en mi justicia.
13 Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.
Mi justicia está cerca, no está lejos; la salvación vendrá rápidamente; y haré libre a Sión, y daré a Israel mi gloria.