< Ishaya 46 >
1 Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
Bel sinketh down; Nebo falleth; Their images are laid upon beasts and cattle; Those that ye once bore are packed upon them; A burden to the weary beast!
2 Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
They sink down; they fall together; They cannot rescue the burden; They themselves go into captivity.
3 “Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
Hearken to me, O house of Jacob, And all the remnant of the house of Israel; Ye that have been borne by me from your birth, That have been carried by me from your earliest breath!
4 Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
Even to your old age I am the same; Even to hoar hairs I will carry you; I have done it, and I will still bear you; I will carry, and will deliver you.
5 “Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
To whom will ye liken me, and compare me? Yea, to whom will ye compare me, that we may be like?
6 Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
They lavish gold out of the bag, And weigh silver in the balance; They hire a goldsmith, and he maketh it a god; They fall down, yea, they worship it.
7 Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
They lift him upon the shoulder, and carry him; They set him in his place, and there he standeth; From his place he moveth not; Yea, one may cry to him, yet doth he not answer, Nor save him out of his distress.
8 “Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
Remember these things, and show yourselves men; Lay them to heart, ye apostates!
9 Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
Remember the former things in ancient times! For I am God, and there is none else; I am God, and there is none like me.
10 Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
Declaring the end from the beginning; From ancient times the things that were not yet done; Saying, My purpose shall stand, And I will do all my pleasure;
11 Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
Calling from the East the eagle, The man that executeth my purpose from a far country; I have spoken it, I will also bring it to pass; I have purposed it, I will also do it.
12 Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
Hearken to me, ye stubborn-hearted, That are far from deliverance!
13 Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.
I have brought near my deliverance; it is not far off; My salvation shall not tarry; I will give to Zion salvation, To Israel, my glory.