< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Ovako govori Gospod pomazaniku svojemu Kiru, kojega držim za desnicu, da oborim pred njim narode i careve raspašem, da se otvoraju vrata pred njim i da ne budu vrata zatvorena:
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
Ja æu iæi pred tobom, i putove neravne poravniæu, vrata mjedena razbiæu i prijevornice gvozdene slomiæu.
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
I daæu ti blago tajno i bogatstvo sakriveno, da poznaš da sam ja Gospod Bog Izrailjev, koji te zovem po imenu.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
Radi sluge svojega Jakova i Izrailja izbranika svojega prozvah te imenom tvojim i prezimenom, premda me ne znaš.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
Ja sam Gospod, i nema drugoga, osim mene nema boga; opasah te, premda me ne znaš,
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
Da bi poznali od istoka sunèanoga i od zapada da nema drugoga osim mene; ja sam Gospod i nema drugoga,
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
Koji pravim svjetlost i stvaram mrak, gradim mir i stvaram zlo; ja Gospod èinim sve to.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
Rosite, nebesa, ozgo, i oblaci neka kaplju pravdom, neka se otvori zemlja i neka rodi spasenjem i zajedno neka uzraste pravda; ja Gospod stvorih to.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Teško onom ko se svaða s tvorcem svojim; crijep s drugim crepovima neka se svaða; ali hoæe li kao reæi lonèaru svojemu: šta radiš? za tvoj posao nema ruku.
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Teško onom ko govori ocu: što raðaš? i ženi: što se poraðaš?
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Ovako veli Gospod svetac Izrailjev i tvorac njegov: pitajte me što æe biti; za sinove moje i za djelo ruku mojih nareðujte mi.
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
Ja sam naèinio zemlju i èovjeka na njoj stvorio, ja sam razapeo nebesa svojim rukama, i svoj vojsci njihovoj dao zapovijest.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Ja ga podigoh u pravdi, i sve putove njegove poravniæu; on æe sazidati moj grad i roblje moje otpustiæe, ne za novce ni za darove, veli Gospod nad vojskama.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
Ovako veli Gospod: trud Misirski i trgovina Etiopska i Savaca ljudi visoka rasta doæi æe k tebi i biti tvoja; za tobom æe pristati, u okovima æe iæi, i tebi æe se klanjati, tebi æe se moliti govoreæi: doista, Bog je u tebi, i nema drugoga Boga.
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Da, ti si Bog, koji se kriješ, Bog Izrailjev, spasitelj.
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
Oni æe se svi postidjeti i posramiti, otiæi æe sa sramotom svikoliki koji grade likove.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
A Izrailja æe spasti Gospod spasenjem vjeènijem, neæete se postidjeti niti æete se osramotiti dovijeka.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
Jer ovako veli Gospod, koji je stvorio nebo, Bog, koji je sazdao zemlju i naèinio je i utvrdio, i nije je stvorio naprazno, nego je naèinio da se na njoj nastava: ja sam Gospod, i nema drugoga.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
Nijesam govorio tajno ni na mraènu mjestu na zemlji, nijesam rekao sjemenu Jakovljevu: tražite me uzalud. Ja Gospod govorim pravdu, javljam što je pravo.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Skupite se i doðite, pristupite svi koji ste se izbavili izmeðu naroda. Ništa ne znaju koji nose drvo od svojega lika i mole se bogu koji ne može pomoæi.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Oglasite, i dovedite, neka vijeæaju zajedno: ko je to od starine kazao? ko je javio još onda? Nijesam li ja, Gospod? Nema osim mene drugoga Boga, nema Boga pravednoga i spasitelja drugoga osim mene.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Pogledajte u mene, i spašæete se svi krajevi zemaljski; jer sam ja Bog, i nema drugoga.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
Sobom se zakleh; izide iz usta mojih rijeè pravedna, i neæe se poreæi, da æe mi se pokloniti svako koljeno, i zaklinjati se svaki jezik,
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
I govoriæe: u Gospodu je pravda i sila; k njemu æe doæi; ali æe se posramiti svi koji se gnjeve na nj.
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
U Gospodu æe se opravdati i proslaviti sve sjeme Izrailjevo.

< Ishaya 45 >