< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
This is what Yahweh says to his anointed, to Cyrus, whose right hand I hold, in order to subdue nations before him, to disarm kings, and to open the doors before him, so that gates remain open:
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
“I will go before you and level the mountains; I will break in pieces the doors of bronze and cut in pieces their iron bars,
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
and I will give you the treasures of darkness and riches hidden away, that you may know that it is I, Yahweh, who call you by your name, I, the God of Israel.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
For Jacob my servant's sake, and Israel my chosen, I have called you by your name, giving you a title of honor, though you have not known me.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
I am Yahweh, and there is no other; there is no God but me. I will arm you for battle, though you have not known me;
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
that people may know from the rising of the sun, and from the west, that there is no god but me: I am Yahweh, and there is no other.
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
I form the light and create darkness; I bring peace and create disaster; I am Yahweh, who does all these things.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
You heavens, rain down from above! Let the skies rain down righteousness. Let the earth absorb it, that salvation may sprout up, and righteousness spring up together with it. I, Yahweh, have created them both.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Woe to anyone who argues with the one who formed him, to him who is like any other earthen pot among all the earthen pots in the ground! Does the clay say to the potter, 'What are you making?' or 'Your work has no handles on it'?
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Woe to him who says to a father, 'What are you fathering?' or to a woman, 'What are you giving birth to?'
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
This is what Yahweh says, the Holy One of Israel, his Maker: 'Why do you ask questions about what I will do for my children? Do you tell me what to do concerning the work of my hands?'
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
'I made the earth and created man on it. It was my hands that stretched out the heavens, and I commanded all the stars to appear.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
I stirred Cyrus up in righteousness, and I will smooth out all his paths. He will build my city; he will let my exiled people go home, and not for price nor bribe,'” says Yahweh of hosts.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
This is what Yahweh says, “The earnings of Egypt and the merchandise of Cush with the Sabeans, men of tall stature, will be brought to you. They will be yours. They will follow after you, coming in chains. They will bow down to you and plead with you saying, 'Surely God is with you, and there is no other except him.'”
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Truly you are a God who hides yourself, God of Israel, Savior.
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
They will all be ashamed and disgraced together; those who carve idols will walk in humiliation.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
But Israel will be saved by Yahweh with an everlasting salvation; you will never again be ashamed or humiliated.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
This is what Yahweh says, who created the heavens, the true God who created the earth and made it, who established it. He created it, not as a waste, but designed it to be inhabited: “I am Yahweh, and there is no other.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
I have not spoken in private, in some hidden place; I did not say to Jacob's descendants, 'Seek me in vain!' I am Yahweh, who speaks sincerely; I declare the things that are right.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Assemble yourselves and come! Gather together, you refugees from among the nations! They have no knowledge, those who carry carved images and pray to gods that cannot save.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Come close and declare it to me, bring the evidence! Let them conspire together. Who has shown this from long ago? Who announced it? Was it not I, Yahweh? There is no God except me, a just God and a Savior; there is no one besides me.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Turn to me and be saved, all the ends of the earth; for I am God, and there is no other.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
By myself I swear, speaking my just decree, and it will not turn back: 'To me every knee will bend, every tongue will swear.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
They will say of me, “In Yahweh alone are salvation and strength.”'” They will all be ashamed who are angry at him.
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
In Yahweh all the descendants of Israel will be justified; they will take pride in him.

< Ishaya 45 >