< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Cyrus is the one whom Yahweh has appointed [to be the emperor of Persia] and to whom he will give great power [IDM]; Yahweh will enable him to defeat other nations and to take away the power of their kings. He will cause gates of cities to be opened, and no one will ever be able to shut them.
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
This is what Yahweh says to him: “Cyrus, I will go ahead of you and level the mountains. I will smash down bronze gates and cut through iron bars.
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
I will give you treasures [that people have hidden] in dark secret places [DOU]. I will do that in order that you will know that I am Yahweh, the God to whom the Israelis belong, the God who calls you by your name.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
I have summoned you, calling out your name, for the sake of [the people of] Israel [DOU] whom I have chosen, who serve me. Even though you do not know me, I will give you a title which has great honor.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
I am Yahweh, and there is no other God [DOU]. Even though you do not know me, I will give you power
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
in order that everyone in the world, from the east to the west, will know that there is no other [God]. I am Yahweh, and there is no other [God].
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
I created the light and the darkness. I cause there to be peace and I cause there to be disasters. I, Yahweh, do all those things.”
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
[And Yahweh also says, “I want my] rescue [of my people] [MET] to fall from the sky like rain. Just like the earth opens wide to accept rain, I will rescue/save my people and cause them to be treated justly. I, Yahweh, am the one who will cause both of those things to happen.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Terrible things will happen to those who argue with me, the one who created them. [They are like] [MET] a clay pot and [I am like] the one who made it; so they certainly cannot [RHQ] criticize me. A lump of clay certainly cannot [RHQ] argue with the one who shapes it [to form a pot], saying, ‘Why are you making me like this?’ The pot cannot say ‘[You have no skill, because] what you made has no handles!’
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
And it would be terrible if an unborn baby would say to its father, ‘Why are you [RHQ] causing me to be born?’ or if it said to its mother, ‘The result of your labor pains will be useless?’”
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Yahweh, the Holy One of the Israeli people, the one who created Israel, says this to them: “(Why do you ask questions about [what I do for you], my children?/You should not ask questions about [what I do for you], my children.) [RHQ] (Why do you tell me about the work that I should do?/You should not tell me about the work that I should do.) [RHQ]
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
I am the one who created the earth and created people to live on it. I stretched out the sky with my hands, and I put the stars in their places.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
And I will appoint Cyrus to do things that are right/just, and I will enable him to do all those things easily [MET]. His [workers] will rebuild my city, and he will free my people who have been (exiled/forced to leave their country). And he will do it without my rewarding/paying him! [Those things will surely happen because] I, the Commander of the armies of angels, have said it.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
And this is [also] what [I], Yahweh, say [to you, my people]: ‘You will rule the people of Egypt and Ethiopia, and the tall people of Seba [in Arabia] will become your slaves. They will come to you bringing all the things that they sell, and it will all be yours. [As prisoners], they will have chains on their arms as they follow you. They will prostrate themselves in front of you and say, “God is with/helping you and he is the only God; there is no other God.” '”
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
God, although we cannot see you, you are the one to whom [we] Israeli people belong, the one who saves us.
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
All those who make idols will be humiliated. They will all be disgraced together.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
But you, Yahweh, will rescue [us, your] Israeli people, and we will be free forever. Never again will we again be humiliated and disgraced.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
Yahweh is God; he is the one who created the sky and created and formed the earth. He did not want it to remain with nothing living on it; he wanted people to live on it. [He says], “I am Yahweh; there is no other [God].
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
[What I proclaimed], I did not speak secretly or [hide what I was saying by speaking] in a dark place. When I spoke to the descendants of Jacob, I did not tell them ‘It will be useless for you to (seek for/pray to) me!’ I, Yahweh, speak [only] what is true and what is right.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
You people who are still alive after experiencing great disasters, should come and gather together [and listen to this]: The people who carry around their wooden idols and pray to them are foolish, because those idols cannot rescue them!
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Talk among yourselves, and decide what you will say to prove that [your praying to idols is good]. [And when you do that, I will ask you], ‘Who predicted long ago [what has now happened]? Did any idol tell you [that those things would happen] [RHQ]?’ No, it was [RHQ] only I, Yahweh, who told you, because I am the only God; there is no other God. I am a God who acts righteously and saves people; there is no other one [who does these things].
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Everyone in the world should ask me to save them, because I am the only God who can do that; there is no other one.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
I have solemnly declared, using my own name; I [SYN] have spoken what is true, and I will never change what I have said: [Some day], everyone [SYN] will bow in front of me, and they will all solemnly promise to be loyal to me.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
They will declare, ‘Yahweh is the one who enables us to live righteously and to be strong.’” And all those who have been angry at him will come to him, and they will be ashamed [for having been angry with him].
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
Yahweh is the only one who will enable [us] Israeli people in the future to defeat our enemies, [and then] we will boast about what he [has done for us].

< Ishaya 45 >