< Ishaya 45 >
1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Thus saith Jehovah to his anointed, To Cyrus, whom I hold by his right hand, To subdue nations before him, And ungird the loins of kings; To open before him the two-leaved gates, And the doors shall not be shut.
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
I will go before thee, And make the high places plain; I will break in pieces the gates of brass, And cut in sunder the bars of iron.
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
I will give thee the treasures of darkness, And hidden riches of secret places, That thou mayst know that I am Jehovah Who calleth thee by name, the God of Israel.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
For the sake of Jacob, my servant, And Israel, my chosen, I have called thee by thy name; I have spoken to thee as a friend, though thou hast not known me.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
I am Jehovah, and none else; There is no God besides me; I have girded thee, though thou hast not known me.
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
That men may know from the rising of the sun, And from the West, that there is none besides me; I am Jehovah, and none else.
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
I form the light, and create darkness; I make peace, and create evil; I, Jehovah, do all these things.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
Pour forth, ye heavens, from above; Ye clouds, shower down prosperity! Let the earth open, and bring forth salvation; Yea, let righteousness spring up together! I, Jehovah, create it.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Woe to him that contendeth with his Maker! A potsherd of the potsherds of the earth! Shall the clay say to him that fashioneth it, What makest thou? Or thy work say of thee, He hath no hands?
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Woe to him that saith to his father, Why dost thou beget? Or to his mother, Why dost thou bring forth?
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Thus saith Jehovah, the Holy One of Israel, and his Maker, Ask of me concerning things to come; My children, the work of my hands, leave them to me!
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
I made the earth, And created man upon it; My hands spread out the heavens, And all their host did I arrange.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
I have raised him up for salvation, And I will make all his ways plain; He shall build my city, and release my captives, Not for price, and not for ransom, Saith Jehovah of hosts.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
Thus saith Jehovah: The wealth of Egypt and the merchandise of the Ethiopians and Sabeans, men of stature, Shall come over to thee, and be thine; They shall follow thee; in chains shall they pass along; They shall fall down to thee, and make supplication to thee: “In thee alone is God, and there is none else; There is no other God.”
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Truly thou art a God that hidest thyself, O God of Israel, the saviour!
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
They shall all be ashamed and confounded, They shall go to confusion together, That are makers of idols.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
But Israel shall be saved by Jehovah with an everlasting salvation; Ye shall never be ashamed, nor confounded.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
For thus saith Jehovah, who created the heavens; The God that formed the earth and made it; he that made it firm; He created it not in vain; he formed it to be inhabited: I am Jehovah, and none else.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
I have not spoken in secret, in a dark place of the earth; I have not said to the race of Jacob, Seek ye me in vain! I, Jehovah, speak truth; I declare that which is right.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Assemble yourselves and come; Gather yourselves together, ye that are escaped of the nations! They are without understanding, who carry about with them the wood of their graven image, And pray to a god that cannot save.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Proclaim ye, and bring them near, And let them take counsel together: Who hath made this known from ancient time? Who hath declared it of old? Is it not I, Jehovah, besides whom there is no God? A God that uttereth truth, and giveth salvation; there is none besides me.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Look to me, and be saved, all ye ends of the earth! For I am God, and there is none else.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
By myself have I sworn, The truth hath gone from my mouth, The word, that shall not return, That to me every knee shall bow, That to me every tongue shall swear.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
“Only in Jehovah,” shall men say, “Is salvation and strength; To him shall come and be put to shame, All that are incensed against him.”
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
Through Jehovah shall all the race of Israel be delivered, And in him shall they glory.